• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Hadaka Ta ‘Yan Agaji A Abuja Ta Gudanar Da Taron Kara Wa Juna Sani

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Kungiyar Hadaka Ta ‘Yan Agaji A Abuja Ta Gudanar Da Taron Kara Wa Juna Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Islamic First Aid Organization” (JIFAO) da ke babban birnin tarayya Abuja ta gabatar da taron kara wa juna sani a karo na hudu.

Kungiyar hadaka na ‘yan agajin dukulallen kungiya ce wacce ta hada da kungiyoyin agaji da suka hada da na Jibwis mai shalkwata a Abuja da Jibwis da ke da shalkwata a garin Jos na Jihar Filato da Fityanul Islam of Nigeria da Jama’atu Nasrul Islam da An’nahada da Ash’shabab da kuma Initiatibe.

  • Bayan Hukuncin Kotu, Dan Takarar Sanata Na APC A Nasarawa Ya Bai Wa Magoya Bayansa Hakuri
  • Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

‘Yan agajin sun samu horo a kan abubuwa da yawa masu matukar muhimanci da suka hada da ayykan agaji shi kansa da zamantakewa da dogaro da kai da neman ilimin addini da na zamani da muhimancin hadin kan al’umma da dai sauransu.

Taron ya samu gudummuwar wasu jami’an gwamnati da kuma masu zaman kansu domin kara sanin makaman aiki. Daga cikin hukumomin da suka bayar da gudummuwar sun hada da rundunar ‘yansandan Nijeriya da hukumar kiyaye hadura da hukumar farin kaya (DSS) da hukumar shigi da fice da hukumar Cibil Defence da hukumar gyaran hali da dai sauransu.

‘Yan agaji sun tabbatar da sun samu horo a wannan haduwa mai inganci, kuma sun shaida cewa wannan karon abin ya za musu kamar shi ne na farko saboda yadda aka karantar da su.

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kungiyar Jibwis da ke Abuja karkashin jagorancin, Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau ita ce ta zo ta daya a gasar fareti da aka yi a wannan hadakar, domin sun buga kafa kai ka ce sojoji ko ‘yansandan Nijeriya ne.

Shugaban JIFAO, Alh. Ahmad Adamu Jingi ya yi kira ga gwamnatin tarayya idan ta tashi daukan ma’aikata musamman a bangaren tsaro ta rika neman ‘yan agaji domin suna da kwarewa a kan harkar tsaro sosai duba da yadda ake koyar da su wannan fannin.

Daraktan Jibwis a Abuja, Alhaji Umar Isma’il wanda ya kasance kwamatan JIFAO, ya ja hankalin ‘yan agaji da su ci gaba da nuna halin da’a kamar yadda aka san su da shi, su kuma dage wajen aiki da abin da aka karantar da su domin samun nasara a wajen Allah.

Taron ya samu halartar manyan malamai da daraktoci gami da sarakuna har ma da sauran al’umma da suka hada da Draktan kungiyar Izala, Alhaji Ahmad Lau da Shugaban majalisar malamai na Abuja, Sheikh Muhammad Auwal mai Gaskiya da

Alh. Abdullahi Abdullmalik Diggi da Sarkin Bwari, Alhaji Muhammad Awwal Musa Ijakoro ll.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan AgajiAbuja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Hukuncin Kotu, Dan Takarar Sanata Na APC A Nasarawa Ya Bai Wa Magoya Bayansa Hakuri

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

Related

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

52 minutes ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

2 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

5 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

7 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

9 hours ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

10 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.