ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Hadaka Ta ‘Yan Agaji A Abuja Ta Gudanar Da Taron Kara Wa Juna Sani

by Leadership Hausa
4 years ago
Abuja

Islamic First Aid Organization” (JIFAO) da ke babban birnin tarayya Abuja ta gabatar da taron kara wa juna sani a karo na hudu.

Kungiyar hadaka na ‘yan agajin dukulallen kungiya ce wacce ta hada da kungiyoyin agaji da suka hada da na Jibwis mai shalkwata a Abuja da Jibwis da ke da shalkwata a garin Jos na Jihar Filato da Fityanul Islam of Nigeria da Jama’atu Nasrul Islam da An’nahada da Ash’shabab da kuma Initiatibe.

  • Bayan Hukuncin Kotu, Dan Takarar Sanata Na APC A Nasarawa Ya Bai Wa Magoya Bayansa Hakuri
  • Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

‘Yan agajin sun samu horo a kan abubuwa da yawa masu matukar muhimanci da suka hada da ayykan agaji shi kansa da zamantakewa da dogaro da kai da neman ilimin addini da na zamani da muhimancin hadin kan al’umma da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Taron ya samu gudummuwar wasu jami’an gwamnati da kuma masu zaman kansu domin kara sanin makaman aiki. Daga cikin hukumomin da suka bayar da gudummuwar sun hada da rundunar ‘yansandan Nijeriya da hukumar kiyaye hadura da hukumar farin kaya (DSS) da hukumar shigi da fice da hukumar Cibil Defence da hukumar gyaran hali da dai sauransu.

‘Yan agaji sun tabbatar da sun samu horo a wannan haduwa mai inganci, kuma sun shaida cewa wannan karon abin ya za musu kamar shi ne na farko saboda yadda aka karantar da su.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Kungiyar Jibwis da ke Abuja karkashin jagorancin, Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau ita ce ta zo ta daya a gasar fareti da aka yi a wannan hadakar, domin sun buga kafa kai ka ce sojoji ko ‘yansandan Nijeriya ne.

Shugaban JIFAO, Alh. Ahmad Adamu Jingi ya yi kira ga gwamnatin tarayya idan ta tashi daukan ma’aikata musamman a bangaren tsaro ta rika neman ‘yan agaji domin suna da kwarewa a kan harkar tsaro sosai duba da yadda ake koyar da su wannan fannin.

Daraktan Jibwis a Abuja, Alhaji Umar Isma’il wanda ya kasance kwamatan JIFAO, ya ja hankalin ‘yan agaji da su ci gaba da nuna halin da’a kamar yadda aka san su da shi, su kuma dage wajen aiki da abin da aka karantar da su domin samun nasara a wajen Allah.

Taron ya samu halartar manyan malamai da daraktoci gami da sarakuna har ma da sauran al’umma da suka hada da Draktan kungiyar Izala, Alhaji Ahmad Lau da Shugaban majalisar malamai na Abuja, Sheikh Muhammad Auwal mai Gaskiya da

Alh. Abdullahi Abdullmalik Diggi da Sarkin Bwari, Alhaji Muhammad Awwal Musa Ijakoro ll.

Abuja
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Labarai

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
Labarai

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.