• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu

by Abubakar Abba
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yansanda a Jihar Koros Ribas sun kama wani dan shekara 49 mai suna Eyo Etim, bisa zarginsa da kashe wata budurwa mai suna Harmony Edemawan a yankin Atim da ke karamar hukumar Akpabuyo.

An ruwaito cewa, wanda ake zargin an cafke shi ne a ranar bikin Kirisimeti.

  • Liverpool Ta Sayi Cody Gakpo Daga PSV
  • Masu Son Gwamnatin Tarayya Ta Yi Magudi A Zaben Bauchi, Ba Za Su Yi Nasara Ba – Bala Mohammed 

Wata majiya a karamar hukumar Akpabuyo, ta shaida wa LEADERSHIP cewa, asirinsa ya tonu ne lokacin da wasu ‘yan sintiri a yankin suka gudanar da bincike a gidansa bayan an samu labarin bacewar budurwar.

A lokacin bincike, ‘yan sintirin sun ga jini a kasa gidan inda suka gayyato ‘yansanda zuwa gidan, nan take ‘yansandan suka bayar da umarnin bude tankin ruwan, inda aka ga gawar budurwar a cikin tankin.

Budurwar dai, ta kasance ma’aikaciya ce a kamfanin Lafarge Holcim, inda kuma bayan gano gawarta, ‘yansandan suka kama Eyo Etim bisa zarginsa da kitsa kashe Edemawan saboda bashin da yake binta.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

An ruwaito cewa, budurwar ta bace ne tun a ranar 22 ga watan Disamba, 2022.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Sule Balarabe, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Eyo na hannunsu a yanzu.

Ya ce, Eyo ya basu bayanan karya na cewa, budurwar ta sayar da wata kadararsa da kudinta ya kai kimanin Naira miliyan tara sannan kuma taki biyansa.

Sule, ya kara da cewa, Eyo ya yi hayar wasu mutane su sace ta don ya karbi kudinsa, amma aka kashe ta aka kuma boye gawarta a cikin tankin ruwan, inda ya ce, ana ci gaba da bincike don a kamo sauran mutanen da hada baki da su don hallaka budurwar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ya ranci bashin budurwar har kimanin Naira miliyan 1.2 wacce kuma aka ce, yana yin soyayya da wata ‘yar uwarta mai suna Ruth Edem ‘yar shekara 22 kuma daliba a jami’ar UNICAL.

Wani dan uwan budurwar da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya ce, Eyo ya ranci kudin budurwar kimanin Naira miliyan 1.2 a farkon wannan shekarar don bunkasa kasuwancinsa na sayar da manja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBincikeBudurwaKisaTankin Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Uwan Juna 3 Bayan Biyan Kudin Fansa A Taraba

Next Post

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

4 months ago
Next Post
CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.