• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu

by Abubakar Abba
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yansanda a Jihar Koros Ribas sun kama wani dan shekara 49 mai suna Eyo Etim, bisa zarginsa da kashe wata budurwa mai suna Harmony Edemawan a yankin Atim da ke karamar hukumar Akpabuyo.

An ruwaito cewa, wanda ake zargin an cafke shi ne a ranar bikin Kirisimeti.

  • Liverpool Ta Sayi Cody Gakpo Daga PSV
  • Masu Son Gwamnatin Tarayya Ta Yi Magudi A Zaben Bauchi, Ba Za Su Yi Nasara Ba – Bala Mohammed 

Wata majiya a karamar hukumar Akpabuyo, ta shaida wa LEADERSHIP cewa, asirinsa ya tonu ne lokacin da wasu ‘yan sintiri a yankin suka gudanar da bincike a gidansa bayan an samu labarin bacewar budurwar.

A lokacin bincike, ‘yan sintirin sun ga jini a kasa gidan inda suka gayyato ‘yansanda zuwa gidan, nan take ‘yansandan suka bayar da umarnin bude tankin ruwan, inda aka ga gawar budurwar a cikin tankin.

Budurwar dai, ta kasance ma’aikaciya ce a kamfanin Lafarge Holcim, inda kuma bayan gano gawarta, ‘yansandan suka kama Eyo Etim bisa zarginsa da kitsa kashe Edemawan saboda bashin da yake binta.

Labarai Masu Nasaba

An Cafke Wadanda Ake Zargin Yi Wa Ma’aikacin PNCH Fashi A Legas

Kotu Ta Yankewa Wasu Matasa 2 Hukuncin Zaman Gidan Yari Kan Gudun Wuce Kima A Kan Dokuna

An ruwaito cewa, budurwar ta bace ne tun a ranar 22 ga watan Disamba, 2022.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Sule Balarabe, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Eyo na hannunsu a yanzu.

Ya ce, Eyo ya basu bayanan karya na cewa, budurwar ta sayar da wata kadararsa da kudinta ya kai kimanin Naira miliyan tara sannan kuma taki biyansa.

Sule, ya kara da cewa, Eyo ya yi hayar wasu mutane su sace ta don ya karbi kudinsa, amma aka kashe ta aka kuma boye gawarta a cikin tankin ruwan, inda ya ce, ana ci gaba da bincike don a kamo sauran mutanen da hada baki da su don hallaka budurwar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ya ranci bashin budurwar har kimanin Naira miliyan 1.2 wacce kuma aka ce, yana yin soyayya da wata ‘yar uwarta mai suna Ruth Edem ‘yar shekara 22 kuma daliba a jami’ar UNICAL.

Wani dan uwan budurwar da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya ce, Eyo ya ranci kudin budurwar kimanin Naira miliyan 1.2 a farkon wannan shekarar don bunkasa kasuwancinsa na sayar da manja.

Tags: 'YansandaBincikeBudurwaKisaTankin Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Uwan Juna 3 Bayan Biyan Kudin Fansa A Taraba

Next Post

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

Related

‘Yansanda Sun kama Wani Babban Dan Damfara A Legas
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wadanda Ake Zargin Yi Wa Ma’aikacin PNCH Fashi A Legas

2 days ago
Kotu Ta Yankewa Wasu Matasa 2 Hukuncin Zaman Gidan Yari Kan Gudun Wuce Kima A Kan Dokuna
Kotu Da Ɗansanda

Kotu Ta Yankewa Wasu Matasa 2 Hukuncin Zaman Gidan Yari Kan Gudun Wuce Kima A Kan Dokuna

1 week ago
NSCDC Ta Kama Barayin Kebur Da Suka Yi Shigar Injiniyoyi A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Kama Barayin Kebur Da Suka Yi Shigar Injiniyoyi A Abuja

3 weeks ago
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Wasu ‘Yansanda Da Laifin Karbar Kudi Da Cin Zarafin Wasu Mutane A Ribas

3 weeks ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

…Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

3 weeks ago
Jami’in LASTMA Na Bogi Da Ya Sato Mota Ya Shiga Hannu
Kotu Da Ɗansanda

Jami’in LASTMA Na Bogi Da Ya Sato Mota Ya Shiga Hannu

4 weeks ago
Next Post
CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

October 2, 2023
Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.