• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Dakwa Ya Aurar Da Samari Da ‘Yanmata Gami Da Nadin Sarautu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labarai
0
Sarkin Dakwa Ya Aurar Da Samari Da ‘Yanmata Gami Da Nadin Sarautu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A safiyar ranar Asabar da ta gabata ce, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, ya aurar da samari da ‘yammata 34, maza 17 mata 17, an gabatar da bikin ne a fadar sarkin da ke Dakwa ta yankin Karamar Hukumar Bwari da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Bikin da ya samu halartar manyan baki daga sassan kasar nan.
Babban bako kuma uba a wurin shi ne, Tsohon Gwamnan Jihar Kano Kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, wanda kuma shi ya zama a matsayin uba ga ‘yammatan wanda shi ya ba da aurensu.

  • Jiga-Jigan NNPP Da PDP Sun Sauya Sheka Zuwa APC A Zamfara 

Wakilin LEADERSHIP Hausa Auwal Mu’azu, ya samu zantawa da Sanatan jim kadan bayan kammala daurin auren inda ya nuna godiya da farin cikinsa da zuwa wannan masarauta, musamman yadda ya ga an tsara gudanar da wannan aure. ” A yau wadannan mutum 34 za su kwana cikin farin ciki, da yawa mutane ba su gane fa’idar irin wannan aure a addinance ba, kuma basu gane shi a zamantakewa ba.

Yau sarki ya tuno min da wacan lokaci da muka yi auren maza da mata sama da dubbai, wanda yau din nan cikin yardar Allah.” In ji shi. Ya yi kira ga shugabanni da masu hannu da shuni da su yi koyi da irin wadannan abubuwan alheri.

A cewarsa wannan tsari ne da zai taimaka wa marasa hali su samu sukunin aurar da ‘ya’yansu, a karshe ya yi addu’ar fatan Allah ya sanya alheri ya kuma zaunar da su lafiya.
Tun da fari a nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, godiya ya yi ga Allah bisa wannan rana mai mhimmanci, kazalika ya yi godiya ga jagoran na Kwankwasiyya bisa amsa gayyatarsa da ya yi, gami da yi masa fatan alheri da addu’ar Allah ya biya masa bukarsa na abubuwan da ya sa gaba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

Shi ma Sabon Sarkin Samarin na Dakwa wanda yana daga Abdurrahman Abdurrashid, wanda aka fi sani da suna Senior, a yanzu Alhamdu lillahi muna godiya ga Allah da ya sa muka kawo wannan lokaci, a yanzu dai an yi min sarauta mai taken Sarkin Samarin Dakwa, Ubangiji Allah ya kai kowa gidansa lafiya, mun gode mun gode Allah ya saka wa kowa da alheri.

Hakika lallai matasa sun ba da gudunmawa sosai, kuma in sha Allahu za mu tsaya kai da fata mu ga duk abubuwan da basu fi karfimmu ba za mu iya tsayawa tsayin daka mu ga mun kare wa matasa hakkinsu, mun gode, mun gode Allah ya saka da alheri. Hakazalika ya yi kira ga matasa da su guji shaye-shaye, domin shaye-shaye ba su da amfani a rayuwa.

” Sannan kuma muma za mu ba da gudunmawar daidai gwargwado domin duk wand aka ji ya lalace to akwai wadanda suka lalata shi, in sha Allahu idan akwai na sama da shi in suka tsawatar masa to zai kokari ya ga daina domin ya ga ya girmama su,”in ji shi.

Bugu da kari ya ja kunnen matasa a duk fadin kasar nan da su ni sanci ‘yan siyasar da za su yi amfani da su wajen basu kayan maye domin su yi bangar siyasa idan zabe ya zo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qin Gang Ya Jaddada Muhimmancin Wanzar Da Daidaito A Dangantakar Sin Da Amurka

Next Post

Bayan Kashe Ma’aikacin CBN Da Matarsa, An Yi Garkuwa Da Dansa A Ogun

Related

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

41 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

3 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

3 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

5 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

6 hours ago
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

14 hours ago
Next Post
kudancin kaduna

Bayan Kashe Ma’aikacin CBN Da Matarsa, An Yi Garkuwa Da Dansa A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.