ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Dakwa Ya Aurar Da Samari Da ‘Yanmata Gami Da Nadin Sarautu

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Sarkin dakwa

A safiyar ranar Asabar da ta gabata ce, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, ya aurar da samari da ‘yammata 34, maza 17 mata 17, an gabatar da bikin ne a fadar sarkin da ke Dakwa ta yankin Karamar Hukumar Bwari da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Bikin da ya samu halartar manyan baki daga sassan kasar nan.
Babban bako kuma uba a wurin shi ne, Tsohon Gwamnan Jihar Kano Kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, wanda kuma shi ya zama a matsayin uba ga ‘yammatan wanda shi ya ba da aurensu.

  • Jiga-Jigan NNPP Da PDP Sun Sauya Sheka Zuwa APC A Zamfara 

Wakilin LEADERSHIP Hausa Auwal Mu’azu, ya samu zantawa da Sanatan jim kadan bayan kammala daurin auren inda ya nuna godiya da farin cikinsa da zuwa wannan masarauta, musamman yadda ya ga an tsara gudanar da wannan aure. ” A yau wadannan mutum 34 za su kwana cikin farin ciki, da yawa mutane ba su gane fa’idar irin wannan aure a addinance ba, kuma basu gane shi a zamantakewa ba.

ADVERTISEMENT

Yau sarki ya tuno min da wacan lokaci da muka yi auren maza da mata sama da dubbai, wanda yau din nan cikin yardar Allah.” In ji shi. Ya yi kira ga shugabanni da masu hannu da shuni da su yi koyi da irin wadannan abubuwan alheri.

A cewarsa wannan tsari ne da zai taimaka wa marasa hali su samu sukunin aurar da ‘ya’yansu, a karshe ya yi addu’ar fatan Allah ya sanya alheri ya kuma zaunar da su lafiya.
Tun da fari a nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, godiya ya yi ga Allah bisa wannan rana mai mhimmanci, kazalika ya yi godiya ga jagoran na Kwankwasiyya bisa amsa gayyatarsa da ya yi, gami da yi masa fatan alheri da addu’ar Allah ya biya masa bukarsa na abubuwan da ya sa gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Shi ma Sabon Sarkin Samarin na Dakwa wanda yana daga Abdurrahman Abdurrashid, wanda aka fi sani da suna Senior, a yanzu Alhamdu lillahi muna godiya ga Allah da ya sa muka kawo wannan lokaci, a yanzu dai an yi min sarauta mai taken Sarkin Samarin Dakwa, Ubangiji Allah ya kai kowa gidansa lafiya, mun gode mun gode Allah ya saka wa kowa da alheri.

Hakika lallai matasa sun ba da gudunmawa sosai, kuma in sha Allahu za mu tsaya kai da fata mu ga duk abubuwan da basu fi karfimmu ba za mu iya tsayawa tsayin daka mu ga mun kare wa matasa hakkinsu, mun gode, mun gode Allah ya saka da alheri. Hakazalika ya yi kira ga matasa da su guji shaye-shaye, domin shaye-shaye ba su da amfani a rayuwa.

” Sannan kuma muma za mu ba da gudunmawar daidai gwargwado domin duk wand aka ji ya lalace to akwai wadanda suka lalata shi, in sha Allahu idan akwai na sama da shi in suka tsawatar masa to zai kokari ya ga daina domin ya ga ya girmama su,”in ji shi.

Bugu da kari ya ja kunnen matasa a duk fadin kasar nan da su ni sanci ‘yan siyasar da za su yi amfani da su wajen basu kayan maye domin su yi bangar siyasa idan zabe ya zo.

Sarkin dakwa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
kudancin kaduna

Bayan Kashe Ma’aikacin CBN Da Matarsa, An Yi Garkuwa Da Dansa A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.