ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Dakwa Ya Aurar Da Samari Da ‘Yanmata Gami Da Nadin Sarautu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Sarkin dakwa

A safiyar ranar Asabar da ta gabata ce, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, ya aurar da samari da ‘yammata 34, maza 17 mata 17, an gabatar da bikin ne a fadar sarkin da ke Dakwa ta yankin Karamar Hukumar Bwari da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Bikin da ya samu halartar manyan baki daga sassan kasar nan.
Babban bako kuma uba a wurin shi ne, Tsohon Gwamnan Jihar Kano Kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, wanda kuma shi ya zama a matsayin uba ga ‘yammatan wanda shi ya ba da aurensu.

  • Jiga-Jigan NNPP Da PDP Sun Sauya Sheka Zuwa APC A Zamfara 

Wakilin LEADERSHIP Hausa Auwal Mu’azu, ya samu zantawa da Sanatan jim kadan bayan kammala daurin auren inda ya nuna godiya da farin cikinsa da zuwa wannan masarauta, musamman yadda ya ga an tsara gudanar da wannan aure. ” A yau wadannan mutum 34 za su kwana cikin farin ciki, da yawa mutane ba su gane fa’idar irin wannan aure a addinance ba, kuma basu gane shi a zamantakewa ba.

ADVERTISEMENT

Yau sarki ya tuno min da wacan lokaci da muka yi auren maza da mata sama da dubbai, wanda yau din nan cikin yardar Allah.” In ji shi. Ya yi kira ga shugabanni da masu hannu da shuni da su yi koyi da irin wadannan abubuwan alheri.

A cewarsa wannan tsari ne da zai taimaka wa marasa hali su samu sukunin aurar da ‘ya’yansu, a karshe ya yi addu’ar fatan Allah ya sanya alheri ya kuma zaunar da su lafiya.
Tun da fari a nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Dakwa Dakta Alasan Baba Chikuri, godiya ya yi ga Allah bisa wannan rana mai mhimmanci, kazalika ya yi godiya ga jagoran na Kwankwasiyya bisa amsa gayyatarsa da ya yi, gami da yi masa fatan alheri da addu’ar Allah ya biya masa bukarsa na abubuwan da ya sa gaba.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Shi ma Sabon Sarkin Samarin na Dakwa wanda yana daga Abdurrahman Abdurrashid, wanda aka fi sani da suna Senior, a yanzu Alhamdu lillahi muna godiya ga Allah da ya sa muka kawo wannan lokaci, a yanzu dai an yi min sarauta mai taken Sarkin Samarin Dakwa, Ubangiji Allah ya kai kowa gidansa lafiya, mun gode mun gode Allah ya saka wa kowa da alheri.

Hakika lallai matasa sun ba da gudunmawa sosai, kuma in sha Allahu za mu tsaya kai da fata mu ga duk abubuwan da basu fi karfimmu ba za mu iya tsayawa tsayin daka mu ga mun kare wa matasa hakkinsu, mun gode, mun gode Allah ya saka da alheri. Hakazalika ya yi kira ga matasa da su guji shaye-shaye, domin shaye-shaye ba su da amfani a rayuwa.

” Sannan kuma muma za mu ba da gudunmawar daidai gwargwado domin duk wand aka ji ya lalace to akwai wadanda suka lalata shi, in sha Allahu idan akwai na sama da shi in suka tsawatar masa to zai kokari ya ga daina domin ya ga ya girmama su,”in ji shi.

Bugu da kari ya ja kunnen matasa a duk fadin kasar nan da su ni sanci ‘yan siyasar da za su yi amfani da su wajen basu kayan maye domin su yi bangar siyasa idan zabe ya zo.

Sarkin dakwa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
kudancin kaduna

Bayan Kashe Ma’aikacin CBN Da Matarsa, An Yi Garkuwa Da Dansa A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.