• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Lashe Zaben Shugaban Kasa – Gwamnan Kwara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Lashe Zaben Shugaban Kasa – Gwamnan Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce, Allah ne kadai zai hana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu lashe zaben shugaban kasa da za a gudanar a wata mai kamawa.

Gwamnan ya ce “Na yi amanna Allah ba zai hana wannan nagartaccen mutumin cimma burinsa ba. Asiwaju Tinubu mutum ne na kwarai wanda ya yi tasiri sosai ga rayukan mutane da daman gaske.”

  • Kungiyar Dalibai Za Ta Shiga Zanga-Zanga Kan Kara Kudin Makaranta A Nijeriya
  • Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

Gwamnan ya kara da cewar “Ina da cikakken kwarin guiwar Tinubu zai lashe zaben shugaban kasa.”

Gwamnan yana wannan bayanin ne a Ilorin, babbar birnin jihar, a wajen taron addu’o’i na musamman da Kungiyar Magoya Bayan Tinubu da Shettima a Arewa ta Tsakiya, ta shirya kan neman nasarar dan takarar a zaben 2023.

Da ya ke samun wakilcin mataimakinsa, Kayode Alabi, gwamna AbdulRazaq ya kara da cewa, “Tinubu mutum ne na kwarai. Shi din nagartaccen mutum ne.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Zan sake nanatawa babu wani abin da zai hana Asiwaju cin zaben shugaban kasa baya ga Allah. Na san irin wadannan mutunen kwarai din, Allah ba ya hana musu dama. Babu wani mutum da ya cika dari bisa dari. Allah ne kawai cikakken da ba ya kuskure.”

“Da zarar ya ci zabe, mu kuma za mu ci zabukan 11 ga watan Maris na gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi.

“Ina rokon masu zabe da su zabi Tinubu, su zabi APC daga kasa har sama.”

Shi ma da ke jawabi, Shugaban kungiyar, Sanata Dayo Adeyeye, ya ce Nijeriya na bukatar agajin Tinubu cikin gaggawa.

Ya ce, tabbas Tinubu zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan da suka shafi na tsaro da tattalin arziki.

Shi kuma jagoran shirya taron, Hon. Oyetunde Ojo, cewa ya yi, “Shafaffu da mai masu juya masu mulki ba za su samu gurbi a gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed ba.”

Ya kara da cewa Tinubu zai gudanar da gwamnati ne mai cike da hangen nesa da bin komai bisa tsari domin sabunta kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbdulrazaqAPCGwamnan KwaraTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dubun Mutumin Da Ya Shirya Sace Mahaifinsa Ta Cika A Kwara

Next Post

Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

15 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

4 days ago
Next Post
2023: APC Ta Yi Sa’a Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa – Buhari 

Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.