• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Yadda Aka Siyasantar Da Cutar Covid-19 Ya Fi Cutar Barna

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Yadda Aka Siyasantar Da Cutar Covid-19 Ya Fi Cutar Barna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, kasar Amurka ta sanar da daukar matakan kayyade shigar baki kasar daga kasar Sin, bisa dalilin da ta bayar na wai “yaduwar cutar a kasar Sin ka iya haifar da sauye-sauyen fasalin cutar”. Amma, ko da gaske ne Amurka ta dauki matakin ne don magance cutar?

A hakika, nau’o’in cutar Covid-19 da yanzu haka ke yaduwa a kasar ta Sin, tuni sun yadu a Amurka da ma sauran wasu kasashen duniya kafin a gano su a kasar Sin. Misali, cutar nau’in BA.5 da ke yaduwa a kasar Sin ta kasance wadda aka fi fuskanta a kasar Amurka a watannin da suka gabata, baya ga cutar nau’in XBB.1.5 da kwanan baya aka gano ta a biranen Shanghai da Hangzhou na gabashin kasar, daidai ta kasance cutar da a halin yanzu taka fi yaduwa a kasar Amurka. A sa’i daya kuma, a yayin da cutar ke yaduwa a fadin duniya, sauye-sauyen fasalin cutar ka iya faruwa ko ina a duniya. Don haka, masana ilmin cututtuka masu yaduwa na kasashe da dama, sun bayyana ra’ayoyinsu na rashin yarda da daukar matakan kayyade shigar baki daga kasar Sin, baya ga kuma wasu hukumomin lafiya da suka hada da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Turai suka bayyana cewa, bai dace ba a kayyade shigar baki daga kasar Sin.

Da haka muke ganin cewa, kasar Amurka na daukar matakin ne don siyasantar da cutar.

In mun waiwayi shekaru uku da suka wuce, za mu ga cewa, gwamnatin kasar Amurka ba ta taba mai da hankalinta a kan daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta ta fannin kadagarkin cutar ba, a maimakon haka ma, tana ta kokarin siyasantar da cutar ne, lamarin da ya sa wannan kasar da ke sahun gaba a duniya ta fannin harkokin kiwon lafiya, ta gamu da munanan hasarorin da bai kamata ba, inda ‘yan kasar sama da miliyan 100 suka harbu da cutar, a yayin da sama da mutanen kasar miliyan 1.08 cutar ta halaka, baya ga kuma yara dubu 250 da suka zama marayu a sakamakon cutar.

Sabanin matakin da Amurka din ta dauka, hukumomin yawon shakatawa, da ofisoshin jakadanci na kasashe da dama da ke kasar Sin a kwanan baya, sun yi maraba da bakin kasar Sin zuwa kasashen su, don fatan ganin babbar kasuwar kasar ta taimaka ga farfado da tattalin arzikinsu, suna kuma fatan hada karfi da karfe tsakanin kasa da kasa, zai fitar da duniya daga mawuyacin halin da ake ciki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burina

Next Post

Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

Related

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar
Daga Birnin Sin

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

17 minutes ago
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

22 minutes ago
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

2 hours ago
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

2 hours ago
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

5 hours ago
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

1 day ago
Next Post
Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

LABARAI MASU NASABA

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.