• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisar wakilai, Shamsudden Danbazau, ya ce alamu sun nuna cewar Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar APC zai doke sauran ‘yan takara domin lashe zaben shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.

  • DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi
  • Ɗan China Da Ake Zargi Da Kisan Ummita Ya Ce Naira Miliyan 60 Ya Kashe Mata 

Danbazau, wanda da ne ga Abdululrahman Danbazau (mai ritaya), tsohon babban hafsan sojin Nijeriya, ya ce tsohon gwamnan Jihar Legas, yana da abin da ake bukata don juya kasar nan.

“Tinubu yana da gogewar da zai fitar da kasar daga halin da take ciki. Shi ne mutumin da yake da gogewar kula da duk wadannan batutuwan da suka shafi ‘yan Nijeriya; zai hada kasar waje daya tare da kawar da tashin hankali da ake fuskanta,” in ji shi.

Ya ce jam’iyyar APC ta riga ta lashe zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Danbazau ya ce an gwada APC kuma an gano cewa tana da gogewa a kasar nan.

“Tinubu shugaba ne mai basira, ba zai yi kasa a gwiwa wajen ganin komai ya saitu a kasar nan,” in ji shi.

Da yake magana kan kalubalen tsaro da kasar nan ke fuskanta, Danbazau, ya ce Nijeriya ta samu ci gaba, inda ya ce ana amfani da jirage marasa matuka, lamarin da ya sanya abubuwa suka fara daidaita.

“Muna bukatar samun karin taswirar kasa na musamman, inda za mu iya aika jirage marasa matuka don kai wa ‘yan ta’adda hari a kowane lungu na kasar nan.

“Daga shekarar 2014 zuwa 2018 na ki zuwa sallar Juma’a saboda tsoron harin bam. Dole ne na kasance a gida ko kuma na salla a bariki, amma tun shekara ta 2016, na soma halartar sallar jam’i a masallatan jama’a.

“An magance kalubalen tsaro kuma za ku ga abin da shugaban kasa ke yi ta hanyar zuba jari mai yawa, samun jiragen sama marasa matuka, yin bincike da tura jami’an sojojinmu zuwa wasu kasashe don koyo dabaru da magance matsalolin tsaro,” in ji shi.

Danbazau ya kara da cewa gwamnatin Buhari ta yi abun a zo a gani a fannin tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuDanbazauTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi

Next Post

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

7 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

19 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

1 day ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
Next Post
Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.