ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Dan majalisar wakilai, Shamsudden Danbazau, ya ce alamu sun nuna cewar Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar APC zai doke sauran ‘yan takara domin lashe zaben shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.

  • DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi
  • Ɗan China Da Ake Zargi Da Kisan Ummita Ya Ce Naira Miliyan 60 Ya Kashe Mata 

Danbazau, wanda da ne ga Abdululrahman Danbazau (mai ritaya), tsohon babban hafsan sojin Nijeriya, ya ce tsohon gwamnan Jihar Legas, yana da abin da ake bukata don juya kasar nan.

ADVERTISEMENT

“Tinubu yana da gogewar da zai fitar da kasar daga halin da take ciki. Shi ne mutumin da yake da gogewar kula da duk wadannan batutuwan da suka shafi ‘yan Nijeriya; zai hada kasar waje daya tare da kawar da tashin hankali da ake fuskanta,” in ji shi.

Ya ce jam’iyyar APC ta riga ta lashe zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Danbazau ya ce an gwada APC kuma an gano cewa tana da gogewa a kasar nan.

“Tinubu shugaba ne mai basira, ba zai yi kasa a gwiwa wajen ganin komai ya saitu a kasar nan,” in ji shi.

Da yake magana kan kalubalen tsaro da kasar nan ke fuskanta, Danbazau, ya ce Nijeriya ta samu ci gaba, inda ya ce ana amfani da jirage marasa matuka, lamarin da ya sanya abubuwa suka fara daidaita.

“Muna bukatar samun karin taswirar kasa na musamman, inda za mu iya aika jirage marasa matuka don kai wa ‘yan ta’adda hari a kowane lungu na kasar nan.

“Daga shekarar 2014 zuwa 2018 na ki zuwa sallar Juma’a saboda tsoron harin bam. Dole ne na kasance a gida ko kuma na salla a bariki, amma tun shekara ta 2016, na soma halartar sallar jam’i a masallatan jama’a.

“An magance kalubalen tsaro kuma za ku ga abin da shugaban kasa ke yi ta hanyar zuba jari mai yawa, samun jiragen sama marasa matuka, yin bincike da tura jami’an sojojinmu zuwa wasu kasashe don koyo dabaru da magance matsalolin tsaro,” in ji shi.

Danbazau ya kara da cewa gwamnatin Buhari ta yi abun a zo a gani a fannin tsaro.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.