ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Dan majalisar wakilai, Shamsudden Danbazau, ya ce alamu sun nuna cewar Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar APC zai doke sauran ‘yan takara domin lashe zaben shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.

  • DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi
  • Ɗan China Da Ake Zargi Da Kisan Ummita Ya Ce Naira Miliyan 60 Ya Kashe Mata 

Danbazau, wanda da ne ga Abdululrahman Danbazau (mai ritaya), tsohon babban hafsan sojin Nijeriya, ya ce tsohon gwamnan Jihar Legas, yana da abin da ake bukata don juya kasar nan.

ADVERTISEMENT

“Tinubu yana da gogewar da zai fitar da kasar daga halin da take ciki. Shi ne mutumin da yake da gogewar kula da duk wadannan batutuwan da suka shafi ‘yan Nijeriya; zai hada kasar waje daya tare da kawar da tashin hankali da ake fuskanta,” in ji shi.

Ya ce jam’iyyar APC ta riga ta lashe zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Danbazau ya ce an gwada APC kuma an gano cewa tana da gogewa a kasar nan.

“Tinubu shugaba ne mai basira, ba zai yi kasa a gwiwa wajen ganin komai ya saitu a kasar nan,” in ji shi.

Da yake magana kan kalubalen tsaro da kasar nan ke fuskanta, Danbazau, ya ce Nijeriya ta samu ci gaba, inda ya ce ana amfani da jirage marasa matuka, lamarin da ya sanya abubuwa suka fara daidaita.

“Muna bukatar samun karin taswirar kasa na musamman, inda za mu iya aika jirage marasa matuka don kai wa ‘yan ta’adda hari a kowane lungu na kasar nan.

“Daga shekarar 2014 zuwa 2018 na ki zuwa sallar Juma’a saboda tsoron harin bam. Dole ne na kasance a gida ko kuma na salla a bariki, amma tun shekara ta 2016, na soma halartar sallar jam’i a masallatan jama’a.

“An magance kalubalen tsaro kuma za ku ga abin da shugaban kasa ke yi ta hanyar zuba jari mai yawa, samun jiragen sama marasa matuka, yin bincike da tura jami’an sojojinmu zuwa wasu kasashe don koyo dabaru da magance matsalolin tsaro,” in ji shi.

Danbazau ya kara da cewa gwamnatin Buhari ta yi abun a zo a gani a fannin tsaro.

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.