• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Zai Doke Atiku Da Obi A Zaben Shugaban Kasa – Danbazau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisar wakilai, Shamsudden Danbazau, ya ce alamu sun nuna cewar Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar APC zai doke sauran ‘yan takara domin lashe zaben shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.

  • DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi
  • Ɗan China Da Ake Zargi Da Kisan Ummita Ya Ce Naira Miliyan 60 Ya Kashe Mata 

Danbazau, wanda da ne ga Abdululrahman Danbazau (mai ritaya), tsohon babban hafsan sojin Nijeriya, ya ce tsohon gwamnan Jihar Legas, yana da abin da ake bukata don juya kasar nan.

“Tinubu yana da gogewar da zai fitar da kasar daga halin da take ciki. Shi ne mutumin da yake da gogewar kula da duk wadannan batutuwan da suka shafi ‘yan Nijeriya; zai hada kasar waje daya tare da kawar da tashin hankali da ake fuskanta,” in ji shi.

Ya ce jam’iyyar APC ta riga ta lashe zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Danbazau ya ce an gwada APC kuma an gano cewa tana da gogewa a kasar nan.

“Tinubu shugaba ne mai basira, ba zai yi kasa a gwiwa wajen ganin komai ya saitu a kasar nan,” in ji shi.

Da yake magana kan kalubalen tsaro da kasar nan ke fuskanta, Danbazau, ya ce Nijeriya ta samu ci gaba, inda ya ce ana amfani da jirage marasa matuka, lamarin da ya sanya abubuwa suka fara daidaita.

“Muna bukatar samun karin taswirar kasa na musamman, inda za mu iya aika jirage marasa matuka don kai wa ‘yan ta’adda hari a kowane lungu na kasar nan.

“Daga shekarar 2014 zuwa 2018 na ki zuwa sallar Juma’a saboda tsoron harin bam. Dole ne na kasance a gida ko kuma na salla a bariki, amma tun shekara ta 2016, na soma halartar sallar jam’i a masallatan jama’a.

“An magance kalubalen tsaro kuma za ku ga abin da shugaban kasa ke yi ta hanyar zuba jari mai yawa, samun jiragen sama marasa matuka, yin bincike da tura jami’an sojojinmu zuwa wasu kasashe don koyo dabaru da magance matsalolin tsaro,” in ji shi.

Danbazau ya kara da cewa gwamnatin Buhari ta yi abun a zo a gani a fannin tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuDanbazauTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Saki Doyin Okupe Bayan Tsare Shi

Next Post

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

13 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

2 days ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

3 days ago
Next Post
Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

Har Kullum Kasar Sin Na Baiwa Afirka Fifiko A Harkokin Diflomasiyyarta

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.