• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Noman Abarba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Ake Noman Abarba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Edo na daya daga cikin jihohin da suka yi fice wajen noman abarba a kasar nan, inda manomanta a jihar suka ce, noma ne da ake samaun kudi.

Sai dai,nomanta na tattare da kalubalen da ba kowane manomi ne zai iysa yin noman nata ba.

  • Bangaren Noma Da Masana’antu Masu Nasaba Sun Kai Kashi 16.05 Na GDPn Sin 

Daya daga cikin manomnata a jihar, Henry Osemwenghogho ya bayyana cewa, suna fuskatar kalubalen rumbuna zamani a jihar na adana ta, inda hakan ke jawo wa manomanta asara bayan sun debe ta.

Sannnan ya kara da cewa sauran kalubalen sun hada da, karancin kudi da rashin hanyoyi masu kyau da za su yi jigilarta zuwa kasuwanni bayan sun debe ta da rashin samun ma’aikata na dindin da za su yi aikinta a gona da sauransu.

A cewar Osemwenghogho a jihar abarba na kara samun kasuwa, musaman ganin cewa, Allah ya albarkanci jihar da kasart noma mai kyau.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Ya kara da cewa, ba wai kawai a kasuwanin jihar Edo ba, tana kuma samun kasuwa a jihar Borno da Kaduna da Abuja da Kano da Legas da Ribers da Enugu da kuma a sauran jihohin da ke kasar nan.

Ya ce, noman abarba bai da wani takamaiman lokacin da ake fara yi, amma akasari ana fara yin noman ne daga watan Fabarairu zuwa na Afirilu.

Osemwenghogho ya kara da cewa, idan manomanta ba su samu damar yinta a sauran kadadarsu ba, za su iya ci gaba da yinta a watan Disamba.

A cewarsa ga wadanda sabbi ne wajen nomanta, da farko ana bukatar su tanadi gona ko kuma su yi hayarta.

Ya kara da cewa ana son su tabbatar da sun yi sharar da kuma kone dukkan wasu hakukuwan da za su iya zame wa amfanin tarnaki.

Ana kuma bukatar su, da su tanadi kudi, don su dauko leburorin da za su yi aikinta a gonar.

Osemwenghogho ya ci gaba da cewa, ana kuma bukatar su da su tabbatar da sun samo ingantancen iri.

Ya kara da cewa, kafin zuwa yanzu ana sayar da tushenta ne daga naira 10,000 zuwa naira 20,000 amma a yanzu farashin ya kai daga naira 50 zuwa naira 100, amma ya danganta da girman da take da shi.

Osemwenghogho ya kuma koka a kan yadda har yanzu ba sa samun wani tallafi daga gwamnati ba, musaman domin su kara bunkasa nomanta a jihar da kuma kasa baki daya.

A cewarsa, koda sun bukaci rance daga hukumomin hada-hadar kudin ba sa samu, inda ya kara da cewa, ya taba neman bukatar rancen amma ba a dauki maganar da wata muhimmaci ba.

Osemwenghogho ya sanar da cewa, ana samun dimin kudaden shiga masu yawa a nomanta, domin ana samun masu sayenta da dama da suke zuwa daga jihar Legas da Abuja da Kaduna da Sakkwato da Ribas da Bayelsa da kuma Kuros Ribas.

Manomin ya bayyana cewa, noman na da sauki sosai domin a koda yaushe, ana samun wadanda suke jiransu saye ta.

“Muna kira ga gwamnatin jihar da ta samar mana da hanyoyi don su dinga sarrafar amfanin da suka noma na abarbar a cikin sauki da kuma samar musu da hanyoyin da za su dinga samun rancen kudin yin nomanta, musamman don su kara fadada fannin na su”.

Ya ce, yana da kadada kimain 30 ta Abarba da suke a ke a yankin Obia ta kudu a jihar ta Edo, inda ya yi nuni da cewa, inda gwamnati za ta samar mana da masana’anta, hakan zai taimaka wajen rage mana asarar da muke yi saboda rashin rumbuna, musamna na zamani na adana ta bayan mun debe ta, hakan zai taimaka mana matuka.

Osemwenghogho ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta samar masu da hanyoyi don su dinga sarafar amfanin da suka noma na Abarbar a cikin sauki da kuma samar masu da hanyoyin da za su dinga samun rancen kudaden yin nomanta, musamman don su kara fadada fannin na su.

Shi ma wani manomin Osayi A. ya dangata gobara a matsayin babban kalubalen da manoman suke fuskanta, inda ya kara da cewa, akasarin manomanta suna yin asarar kadadar nomansu saboda kalubalen na gobara da kuma sauran kalubalen da fannin ke fuskantar.

Ya kara da cewa, har ila yau ana kuma fusknatar kalubalen canjin yanayi, inda hakan ke janyo fannin babbar illa.

Osayi ya kara da cewa, fannin na noman Abarba, ana samun kudaden shiga masu yawa, amma sai in har idan manomi ya ci gaba da bata kulawar data dace har zuwa lokacin girbe ta, mussaman wajen yawan cire ciyawa a gonar da aka nomata.

Ya ce, idan ka shuka ta a farkon shekara ana son ka ci gaba da nome ciyar da ke cikin gonar domin ta na da saurin fito wa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Yi Bankwana Da Jami’anta 7 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Kaduna

Next Post

Abdulaziz Abdulaziz Ya Zama Kakakin Bola Ahmad Tinubu

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 days ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 days ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 weeks ago
Next Post
Abdulaziz Abdulaziz Ya Zama Kakakin Bola Ahmad Tinubu

Abdulaziz Abdulaziz Ya Zama Kakakin Bola Ahmad Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

July 7, 2025
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

July 7, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.