ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

by Abubakar Abba
9 months ago
Kifi

Gwamnatin tarayya ta yi hadaka da Hukumar Kula da Abinci da Ayyukan Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO), ta hanyar kaddamar da shirin da za a kashe kimanin Naira miliyan 200, domin kara habaka kiwon kifi a fadin wannan kasa.

Manufar kaddamar da shirin ita ce, domin samar da wadataccen kifi a fadin Nijeriya baki-daya.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Darakta a sashen kula da kiwon kifi a Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, Wellington Omoragbon, a jawabinsa a wajen kaddamar da shirin a yankin Eriwe da ke Jihar Ogun ya sanar da cewa, an kaddamar da shirin a karkashin aikin kiwon kifi na ‘FISH4ACP’.

ADVERTISEMENT

Omoragbon, wanda Darakta na biyu a ma’aikatar ya wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, manufar shirin ita ce, domin a kara samar da kudade a fannin da kumakokarin ci gaba da gudanar da kiwon na kifi a wannan kasa.

Kazalika, ya yaba wa Hukumar ta FAO da kuma sauran abokan hadaka, bisa tallafa wa kasar nan, musamman ta fuskar kara habaka harkokin kiwon kifin.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ya kara da cewa, duba da irin dimbin Kogunan da ake da su a wannan kasa, idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, za a iya bunkasa fannin na kamun kifi a Nijeriya.

Omoragbon ya ci gaba da cewa, kalubalen da ake ci gaba da fuskanta a halin yanzu shi ne, na karancin kudade da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kifin, wanda wannnan babban kalubale ne da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta a kasar.

“Muna sane da cewa, babban kalubalen da masu sana’ar a kasar nan ke ci gaba da fuskanta shi ne, karancin kudade tare da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin kifin, amma za mu iya kokarinmu, domin ganin mun samar wa da masu kiwon dauki, musamman domin a cike gibin da ake da shi a fannin,” a cewar Omoragbon.

hi kuwa a nasa jawabin, wakilin hukumar ta FAO a kasar nan da kuma yankin Afirka ta yamma, Koffy Kokako, kira ya yi da a dauki matakan da suka dace, domin kawo karshen shigo da kifi kimanin tan miliyan biyu da ake yi daga kasashen waje zuwa cikin wannan kasa.

Ya bayyana cewa, tarayyar turai da sauran abokan hadaka; sun zuba kudaden ne, domin masu kiwon kifi a kasar, su samu damar samun kudaden da za su yi kiwon kifin tare kuma da kara bunkasa kiwon kifin a kasar.

Haka nan, ya kara da cewa, a kashi na farko na aikin masu kiwon kifi guda 40 ne aka bai wa daga Naira miliyan 2.5 zuwa Naira miliyan biyar, wanda jimillar kudin suka kai kimanin Naira miliyan 200.

Kifi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.