ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Noman Abarba

by Abubakar Abba
3 years ago
Noman abarba

Jihar Edo na daya daga cikin jihohin da suka yi fice wajen noman abarba a kasar nan, inda manomanta a jihar suka ce, noma ne da ake samaun kudi.

Sai dai,nomanta na tattare da kalubalen da ba kowane manomi ne zai iysa yin noman nata ba.

  • Bangaren Noma Da Masana’antu Masu Nasaba Sun Kai Kashi 16.05 Na GDPn Sin 

Daya daga cikin manomnata a jihar, Henry Osemwenghogho ya bayyana cewa, suna fuskatar kalubalen rumbuna zamani a jihar na adana ta, inda hakan ke jawo wa manomanta asara bayan sun debe ta.

ADVERTISEMENT

Sannnan ya kara da cewa sauran kalubalen sun hada da, karancin kudi da rashin hanyoyi masu kyau da za su yi jigilarta zuwa kasuwanni bayan sun debe ta da rashin samun ma’aikata na dindin da za su yi aikinta a gona da sauransu.

A cewar Osemwenghogho a jihar abarba na kara samun kasuwa, musaman ganin cewa, Allah ya albarkanci jihar da kasart noma mai kyau.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ya kara da cewa, ba wai kawai a kasuwanin jihar Edo ba, tana kuma samun kasuwa a jihar Borno da Kaduna da Abuja da Kano da Legas da Ribers da Enugu da kuma a sauran jihohin da ke kasar nan.

Ya ce, noman abarba bai da wani takamaiman lokacin da ake fara yi, amma akasari ana fara yin noman ne daga watan Fabarairu zuwa na Afirilu.

Osemwenghogho ya kara da cewa, idan manomanta ba su samu damar yinta a sauran kadadarsu ba, za su iya ci gaba da yinta a watan Disamba.

A cewarsa ga wadanda sabbi ne wajen nomanta, da farko ana bukatar su tanadi gona ko kuma su yi hayarta.

Ya kara da cewa ana son su tabbatar da sun yi sharar da kuma kone dukkan wasu hakukuwan da za su iya zame wa amfanin tarnaki.

Ana kuma bukatar su, da su tanadi kudi, don su dauko leburorin da za su yi aikinta a gonar.

Osemwenghogho ya ci gaba da cewa, ana kuma bukatar su da su tabbatar da sun samo ingantancen iri.

Ya kara da cewa, kafin zuwa yanzu ana sayar da tushenta ne daga naira 10,000 zuwa naira 20,000 amma a yanzu farashin ya kai daga naira 50 zuwa naira 100, amma ya danganta da girman da take da shi.

Osemwenghogho ya kuma koka a kan yadda har yanzu ba sa samun wani tallafi daga gwamnati ba, musaman domin su kara bunkasa nomanta a jihar da kuma kasa baki daya.

A cewarsa, koda sun bukaci rance daga hukumomin hada-hadar kudin ba sa samu, inda ya kara da cewa, ya taba neman bukatar rancen amma ba a dauki maganar da wata muhimmaci ba.

Osemwenghogho ya sanar da cewa, ana samun dimin kudaden shiga masu yawa a nomanta, domin ana samun masu sayenta da dama da suke zuwa daga jihar Legas da Abuja da Kaduna da Sakkwato da Ribas da Bayelsa da kuma Kuros Ribas.

Manomin ya bayyana cewa, noman na da sauki sosai domin a koda yaushe, ana samun wadanda suke jiransu saye ta.

“Muna kira ga gwamnatin jihar da ta samar mana da hanyoyi don su dinga sarrafar amfanin da suka noma na abarbar a cikin sauki da kuma samar musu da hanyoyin da za su dinga samun rancen kudin yin nomanta, musamman don su kara fadada fannin na su”.

Ya ce, yana da kadada kimain 30 ta Abarba da suke a ke a yankin Obia ta kudu a jihar ta Edo, inda ya yi nuni da cewa, inda gwamnati za ta samar mana da masana’anta, hakan zai taimaka wajen rage mana asarar da muke yi saboda rashin rumbuna, musamna na zamani na adana ta bayan mun debe ta, hakan zai taimaka mana matuka.

Osemwenghogho ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta samar masu da hanyoyi don su dinga sarafar amfanin da suka noma na Abarbar a cikin sauki da kuma samar masu da hanyoyin da za su dinga samun rancen kudaden yin nomanta, musamman don su kara fadada fannin na su.

Shi ma wani manomin Osayi A. ya dangata gobara a matsayin babban kalubalen da manoman suke fuskanta, inda ya kara da cewa, akasarin manomanta suna yin asarar kadadar nomansu saboda kalubalen na gobara da kuma sauran kalubalen da fannin ke fuskantar.

Ya kara da cewa, har ila yau ana kuma fusknatar kalubalen canjin yanayi, inda hakan ke janyo fannin babbar illa.

Osayi ya kara da cewa, fannin na noman Abarba, ana samun kudaden shiga masu yawa, amma sai in har idan manomi ya ci gaba da bata kulawar data dace har zuwa lokacin girbe ta, mussaman wajen yawan cire ciyawa a gonar da aka nomata.

Ya ce, idan ka shuka ta a farkon shekara ana son ka ci gaba da nome ciyar da ke cikin gonar domin ta na da saurin fito wa.

Noman abarba
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Abdulaziz Abdulaziz Ya Zama Kakakin Bola Ahmad Tinubu

Abdulaziz Abdulaziz Ya Zama Kakakin Bola Ahmad Tinubu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.