• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga 4 Da Cafke Matar Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Makamai A Kaduna

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
An Kashe ‘Yan Bindiga 4 Da Cafke Matar Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Makamai A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta ce, jami’anta sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga guda hudu (4) a musayar wuta da suka yi da su da kama wata mata da take musu safarar bindigogi da alburusai a jihar Kaduna.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na hukumar reshen jihar Kaduna, DSP Muhammed Jalige, ya shaida ta cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutun 3, Sun Sace 30 A Jihar Neja

Jalige ya ce, nasarar ta biyo bayan kokarin jami’an ‘yan sanda na STS da hadin guiwar sojojin Operation Yaki suka samu wurin kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga, inda a ranar 15 ga watan Yuni suka cafke wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne a kan hanyar Saminaka zuwa Jos.

Ya ce, an kama ‘yan bindigan ne a cikin wata mota kirar Sharon mai launin bulu tare da matukinta mai suna James Dawi Dan shekara 31 a duniya mazaunin yankin Vom da ke Kudancin jihar Filato.

Ya kara da cewa a wannan yanayin da suka tabbatar ba za su iya tsallake tarkon jami’an tsaron ba gami da kokarinsu na kai bindigogi ga abokan cin burminsu, nan take suka bude ruwan harsasai ga jami’an tsaron.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Jami’in yada labaran ya ci gaba da cewa, cikin dabarun na aiki da kwarewa, jami’an tsaron sun samu nasarar harbin hudu daga cikin ‘yan bindigan kana an kwashesu zuwa asibitin koyarwa ta Barau Dikko da ke Kaduna inda likita ya tabbatar da mutuwarsu.

Ya ce, sun samu nasarar kwato wasu makamai daga wajen ‘yan bindigan bayan da aka sha karfinsu, “A yayin artabun an kama wata mace da ake bincikenta ta tabbatar da kanta cewa tana safaran bindigogi da alburusai ga ‘yan bindiga a yankin Kaduna.”

Ya ce, bincike dai na cigaba da gudana domin dakile aniyar bata-garin da suka addabi Kaduna da garkuwa da mutane da fashi da makami.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Jumu’a

Next Post

SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

1 week ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

3 weeks ago
Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin ÆŠaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya ÆŠauke Shi

1 month ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

2 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri FyaÉ—e A Bauchi

3 months ago
Next Post
SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya BuÆ™aci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.