ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja

A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.

by Muhammad
4 years ago
Sun

An yi wa mutane uku yankan rago yayin da aka yi garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba a daren Laraba a unguwar Maguzawa da ke karamar hukumar Rafi a jihar Neja.

Rahotanni da dama daga yankin sun ce daga cikin wadanda aka sace akwai mata da kananan yara yayin da mazauna yankin da dama suka tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma garin Birnin Gwari a jihar Kaduna.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,
  • ‘Yan Boko Haram 204 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Jihar Borno

Maguzawa dai yana da tazarar kilomita 25 daga garin Kagara a jihar Neja da kuma kilomita 12 daga Birnin Gwari a jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Hare-haren na Maguzawa ya zo ne kasa da sa’o’i 48 a lokacin da ‘yan bindiga suka kai wani hari a kauyen Gidigore da ke karamar hukumar Rafi, a daren ranar Talata, inda aka kashe akalla rayuka biyar tare da sace wasu da dama.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta ce, “A Maguzawa, an kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba, wasu kuma sun gudu. Ya zuwa yanzu mun ga gawarwaki uku da aka yanka su. Ba mu san adadin mutanen da suka tafi tare da su ba a yanzu. ”

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

Mazauna yankin sun shaida cewa, makwanni uku da suka gabata an yi garkuwa da wasu a karamar hukumar Rafi da da yi musu fashi.

Wani mazaunin garin Ibrahim Ahmad ya ce dan uwansa na daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a daren ranar Talata, inda ya ce mutane da dama sun tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma kona Gwari a jihar Kaduna.

“A cikin kasa da makonni uku, mun ga hare-hare daban-daban har guda 10 a kan mutane daban-daban a karamar hukumar Rafi, kusan kowace rana.

Kafin harin na ranar Talata, makonni biyu da suka gabata, ‘yan bindiga sun kai hari a kauyukan Gulbi, Unguwan-Jaye da Kusherki inda aka kashe mutane 8 tare da yin garkuwa da wasu 36 yayin da mutum daya da ya samu munanan raunuka. A yayin da nake magana da ku, sun bukaci Naira miliyan 50 ga mutanen farko da suka yi garkuwa da su,” inji shi.

Ahmad ya ce an kona gidaje da kadarori na manoma da dama a harin na ranar Talata wanda ya dauki sa’o’i da dama.

Ya bukaci tallafin jin kai daga gwamnati, kungiyoyi da daidaikun jama’a musamman kayan abinci da yara kan sanyawa don rage musu kuncin rayuwa.

Al’umar Gidigore da aka kai harin na baya-bayan nan na da tazarar kilomita kadan daga garin Birnin Gwari na jihar Kaduna, inda ‘yan bindigar suka kai hare-hare da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin na Didigore amma har yanzu bai tabbatar da sabon harin ba.

Ya ce, “A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.”

Sun
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya
Manyan Labarai

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Labarai

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Next Post
Sun

2023: Atiku Ya Gabatar Da Gwamnan Delta, Okowa A Matsayin Mataimakinsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.