• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar “Zomo” Dake Samar Da Yanayi Mai Armashi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shekarar “Zomo” Dake Samar Da Yanayi Mai Armashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wadannan kwanaki, Sinawa suna murnar bikin sabuwar shekara ta gargajiyarsu, wanda ake kira “bikin bazara”. Don taya murnar bikin, wani abokina dake Kano ya buga mana waya a jiya. Ya fahimci al’adun kasar Sin sosai, don haka ya san Sinawa na yin amfani da zagayowar wasu dabbobi 12, wajen wakiltar shekaru daban daban. Ya ce mana: “Ina taya Sinawa murnar sabuwar shekara ta Zomo, da fatan kowa zai kasance cikin koshin lafiya, da iya gudu cikin sauri, kamar yadda zomo yake.”

Ina godiya sosai bisa fatan alheri da aka yi mana, kana na ga wasu abubuwa suna “gudu cikin sauri” a nan kasar Sin, kamar dai yadda wannan aboki ya fada.

  • Ko Kun San Irin Bakar Wuyar Da Ake Sha Wajen Tantance Gawarwaki A Yakin Ukraine?

Da farko, annobar COVID-19 nau’in Omicron na “gudu”, inda ake sa ran ganin bayanta cikin sauri a nan kasar Sin.

Bisa alkaluman da cibiyar kandagarkin cututtuka ta kasar Sin ta bayar, an ce an samu mafi yawan mutanen da suka nemi samun jinya a asibiti a kewayen ranar 22 ga watan Disamban bara, inda yawansu ya kai miliyan 2 da dubu 867 a duk rana. Daga baya jimillar ta fara raguwa. Zuwa ranar 23 ga watan da muke ciki, jimillar ta sauka zuwa dubu 110, wato ta ragu da kashi 96.2%.

Kar mu manta, ana samun mafi yawan zirga-zirgar mutane a lokacin bikin bazara a kasar Sin, musamman ma ta la’akari da yadda kasar ta sassauta matakan kandagarkin yaduwar cutar COVID tun daga karshen bara, inda ko a ranar 24 ga wata kadai, aka samu fasinjoji fiye da miliyan 29 da suka yi zirga-zirga a kasar, adadin da ya karu da kashi 67.3% bisa makamancin lokacin bara. Amma duk da haka, kwararar mutane ba ta tsananta yanayin bazuwar COVID ba. Hakan ya nuna cewa, matakan hana yaduwar annoba da aka daidaita su, sun yi amfani.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Na biyu shi ne, bayan da yanayin annoba ya yi sauki, tattalin arziki ma na farfadowa cikin karin sauri.

A wadannan kwanaki, na ziyarci cibiyoyin kasuwanci na Beijing, da wuraren cin abinci, da kallon sinima, da sauran nune-nune, inda na ga ko ina na cike da mutane, kana suna kokarin sayayya da kashe kudi. Alkaluman da hukumar kasuwanci ta birnin Beijing ta gabatar sun nuna cewa, daga ranar 21 zuwa ta 24 ga wata, wato cikin kwanaki 4 kacal, darajar kayayyaki da abinci da aka sayar da su a birnin Beijing ta kai Yuan biliyan 2.84, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 420.

Kana wannan yanayi mai armashi ya bazu a wurare daban daban. Bisa abun da na gani a telabijin, a duk wani gari na kasar Sin, ana samun cunkuson mutane a wuraren shakatawa, inda ‘yan kasuwa ke shan aiki, suna farin ciki bisa dimbin ribar da suka samu. To, yadda aka samu farawar sabuwar shekara kamar haka, ya nuna yadda tattalin arzikin kasar zai samu ci gaba cikin karin sauri a wannan shekarar da muke ciki.

Har yanzu ban manta da bikin bazara na shekaru 3 da suka wuce ba. Inda a ranar 23 ga watan Janairun shekarar 2020, birnin Wuhan da aka samu barkewar annobar COVID-19 a cikin sa, ya sanar da killace kansa, kana wurare daban daban na kasar Sin suka fara tura mutane da kayayyakin da ake bukata zuwa birnin don ba shi taimako. A lokacin, na soke shirin ziyara, inda ni da iyali na muka kasance a gida don magance kamuwa da cuta.

Sa’an nan a shekaru 2 da suka biyo baya, an ci gaba da daukar tsauraran matakan kandagarkin cuta a nan kasar Sin. Inda mutanen kasar suka yi kokarin hana yaduwar cutar COVID-19, bisa hadin gwiwa, da da’a, da jajircewa, don kare rayukan jama’a daga mummunar cutar mai kisa. Ana ci gaba da wannan kokari, har zuwa karshen shekarar bara, lokacin da aka samu cikar sharudan sassauta matakan kandagarkin cuta.

Saboda haka a wannan bikin bazara, Sinawa sun samu cikakkiyar damar jin dadin haduwa da iyalai, da ziyara a wurare daban daban. Sai dai an fi samun sauyawa cikin zukatansu, inda tsoron kamuwa da cuta ya ragu sosai, kana imani game da makoma mai haske ya karfafa.

Burina shi ne, wannan imani na Sinawa zai taimakawa karfafa gwiwar mutanen kasashe daban daban, kana ci gaban tattalin arzikin Sin zai sa tattalin arzikin duniya samun farfadowa cikin matukar sauri, har ma ya fi saurin gudu na zomo, a wannan shekara ta zomo da muke ciki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19

Next Post

2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Related

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

36 minutes ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

2 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

3 hours ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

4 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

22 hours ago
Next Post
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

2023: INEC Da 'Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

August 7, 2025
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

August 7, 2025
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

August 7, 2025
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.