ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

by Sulaiman
12 months ago
Kansa

An ware ranar 27 ga watan Yulin kowace shekara ne don wayar da kan jama’a game da haɗari da kuma hanyoyin kauce ma kamuwa da mummunar cutar nan ta Kansar Kai da Maƙogwaro.

 

Wannan wayar da kai da masana cutar ta duniya ta shirya a kowace irin wannan rana, ta zama wajibi ne bisa la’akari da cewa ita wannan cuta ta fi sauƙin magani, tare da kawar da ita daga jikin mutum ne kawai idan an gano ta da wuri, amma idan abin ya girma, har ta fantsama, to tana da wuyar magani.

ADVERTISEMENT
  • Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
  • Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

Hakan ne ta sa aka zabi wannan rana domin a wayar wa da jama’a kai game da hanyoyin da za su bi wajen kare kan su daga kamuwa da cutar, wanda hakan zai taimaka wajen rage yaɗuwar ta.

 

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.

 

Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.

 

Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.

 

“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”

 

Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.

 

Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”

Kansa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Kansa

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Kansa

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.