• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Samar Da Fasfo Kimanin Miliyan 2 A Shekarar 2022 —Gwamnatin Tarayya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Samar Da Fasfo Kimanin Miliyan 2 A Shekarar 2022 —Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ce, akalla Fasfo Miliyan 1.9 hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) ta samar a shekarar 2022 da ta gabata, da ke nuna an samu ci gaba da kusan kashi 80 cikin 100 kan wanda aka samar a 2021.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya shaida hakan a ranar Litinin yayin kaddamar da ofishin karba da shigar da bayanan Fasfo da ke Alimosho a Jihar Legas.

  • Shugaba Buhari Ya Karrama CGI Isah Jere Da Lambar Yabo Ta Ƙasa Bisa Mutunta Ɗan’adam A Shugabancinsa
  • Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

An samar da ofishin ne a wani mataki na samar da dabarun tabbatar da aikin Fasfo don tafiya cikin sauki da hanzari ga ‘Yan Nijeriya.

Ministan ya kuma ce, hakan zai rage wahalhalun da ake sha wajen aikin Fasfo a Legas.

“Mun dukufa wajen fadada ayyukanmu na samar da Fasfo domin cike gibin karancin da ake yawan samu a manyan birane musamman irin su Legas. Wannan dalilin ne ya sanya aka samar da ofishin Fasfo a Alimosho da zai rage nauyi ga wasu ofisoshin Fasfo uku da suke Legas.”

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Aregbesola ya kara da cewa, NIS na aiki tukuru wajen kara himma da azama a bangaren samar da Fasfo domin biyan bukatun masu nema da shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

“Bukatun Fasfo na karuwa duk shekara sakamakon yadda ‘Yan Nijeriya da dama ke bukatar fita kasashen waje da kuma wadanda suke son mallakar Fasfo din a matsayin shaida.

“Amma mun kara yawan wuraren yin aikin. A shekarar da ta gabata mun kuma samar da Fasfo Miliyan 1.9, sabanin miliyan 1 da muka samar a 2021.”

Ministan ya yi karin hasken cewa ofishin da aka bude a Alimosho zai rika amsar zallar bukatun masu neman fasfo, amma ba wai waje ne da za a rika wallafa fasfon ba.

Duk da hakan ministan ya ce akwai bukatar kara samar da wasu ofisoshin yin Fasfo a kalla guda 15 a Legas sakamakon cewa jihar ita ce take da kusan rabin dukkan fasfon da ake gabatar da bukatar nema a Nijeriya.

Aregbesola ya kuma jadadda cewa babu makawa a shigar da kamfanoni masu zaman kansu wajen samar da wadannan ofisoshin na karba da shigar da bayanan fasfo a Legas, saboda kalubalen kudade da gwamnati ke fuskanta, domin hakan zai rage tsawon lokacin da ake kwashe wajen jiran fasfo.

“Amma saboda kalubalen kudade, gwamnati bata iya samar da wadannan ofisoshi, don haka za mu bukaci abokan hulda masu zaman kansu da za su samar da ofishin, abin da kawai za su yi shi ne samar da ofisoshin amma jami’an shige da fice ne za su rika kula da su tare da gudanar da su.

“Tabbas muna bukatar karin wannan a Legas. Hakan ya faru ne saboda rabin duk takardun fasfo ana yin su ne a Legas.”
Aregbesola ya kuma yi kira ga masu bukatar fasfo da su rika yi da kansu a ofisoshin NIS ba tare da mu’amala da marasa gaskiya ba.

Tun da farko dai, Aregbesola ya kaddamar da hedikwatar hukumar shige da fice ta Nijeriya (NIS) reshen Jihar Legas da ke Ikoyi.

Ya bayyana cewa kaddamar da ofishin na daya daga cikin ci gaban da ma’aikatar harkokin cikin gida ta samar a karkashin gwamnatin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Tun da aka nada ni a matsayin minista, mun kaddamar da sabbin hedikwatocin jihohi 17 a fadin kasar nan na hukumar NIS, inda ta Legas ita ce ta 18.

Kokarin da gwamnatin Shugaba, Muhammadu Buhari, take yi na ganin an kara tabbatar da tsaron iyakokinmu ya sa aka samar da sabbin ofisoshi na kula da sintiri da inganta Tsarin Kula da Iyakoki na zamani bisa doka”. In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JereNISShige Da Fice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Next Post

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

2 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

2 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

2 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

5 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

7 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

22 hours ago
Next Post
Ba Za Mu Yi Kasa A Guiwa Wajen Tabbatar Da Ingantaccen Aiki Ga Al’umma Ba – Shugaban NIS

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.