ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Samar Da Fasfo Kimanin Miliyan 2 A Shekarar 2022 —Gwamnatin Tarayya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Gwamnatin tarayya ta ce, akalla Fasfo Miliyan 1.9 hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) ta samar a shekarar 2022 da ta gabata, da ke nuna an samu ci gaba da kusan kashi 80 cikin 100 kan wanda aka samar a 2021.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya shaida hakan a ranar Litinin yayin kaddamar da ofishin karba da shigar da bayanan Fasfo da ke Alimosho a Jihar Legas.

  • Shugaba Buhari Ya Karrama CGI Isah Jere Da Lambar Yabo Ta Ƙasa Bisa Mutunta Ɗan’adam A Shugabancinsa
  • Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

An samar da ofishin ne a wani mataki na samar da dabarun tabbatar da aikin Fasfo don tafiya cikin sauki da hanzari ga ‘Yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ministan ya kuma ce, hakan zai rage wahalhalun da ake sha wajen aikin Fasfo a Legas.

“Mun dukufa wajen fadada ayyukanmu na samar da Fasfo domin cike gibin karancin da ake yawan samu a manyan birane musamman irin su Legas. Wannan dalilin ne ya sanya aka samar da ofishin Fasfo a Alimosho da zai rage nauyi ga wasu ofisoshin Fasfo uku da suke Legas.”

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Aregbesola ya kara da cewa, NIS na aiki tukuru wajen kara himma da azama a bangaren samar da Fasfo domin biyan bukatun masu nema da shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

“Bukatun Fasfo na karuwa duk shekara sakamakon yadda ‘Yan Nijeriya da dama ke bukatar fita kasashen waje da kuma wadanda suke son mallakar Fasfo din a matsayin shaida.

“Amma mun kara yawan wuraren yin aikin. A shekarar da ta gabata mun kuma samar da Fasfo Miliyan 1.9, sabanin miliyan 1 da muka samar a 2021.”

Ministan ya yi karin hasken cewa ofishin da aka bude a Alimosho zai rika amsar zallar bukatun masu neman fasfo, amma ba wai waje ne da za a rika wallafa fasfon ba.

Duk da hakan ministan ya ce akwai bukatar kara samar da wasu ofisoshin yin Fasfo a kalla guda 15 a Legas sakamakon cewa jihar ita ce take da kusan rabin dukkan fasfon da ake gabatar da bukatar nema a Nijeriya.

Aregbesola ya kuma jadadda cewa babu makawa a shigar da kamfanoni masu zaman kansu wajen samar da wadannan ofisoshin na karba da shigar da bayanan fasfo a Legas, saboda kalubalen kudade da gwamnati ke fuskanta, domin hakan zai rage tsawon lokacin da ake kwashe wajen jiran fasfo.

“Amma saboda kalubalen kudade, gwamnati bata iya samar da wadannan ofisoshi, don haka za mu bukaci abokan hulda masu zaman kansu da za su samar da ofishin, abin da kawai za su yi shi ne samar da ofisoshin amma jami’an shige da fice ne za su rika kula da su tare da gudanar da su.

“Tabbas muna bukatar karin wannan a Legas. Hakan ya faru ne saboda rabin duk takardun fasfo ana yin su ne a Legas.”
Aregbesola ya kuma yi kira ga masu bukatar fasfo da su rika yi da kansu a ofisoshin NIS ba tare da mu’amala da marasa gaskiya ba.

Tun da farko dai, Aregbesola ya kaddamar da hedikwatar hukumar shige da fice ta Nijeriya (NIS) reshen Jihar Legas da ke Ikoyi.

Ya bayyana cewa kaddamar da ofishin na daya daga cikin ci gaban da ma’aikatar harkokin cikin gida ta samar a karkashin gwamnatin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Tun da aka nada ni a matsayin minista, mun kaddamar da sabbin hedikwatocin jihohi 17 a fadin kasar nan na hukumar NIS, inda ta Legas ita ce ta 18.

Kokarin da gwamnatin Shugaba, Muhammadu Buhari, take yi na ganin an kara tabbatar da tsaron iyakokinmu ya sa aka samar da sabbin ofisoshi na kula da sintiri da inganta Tsarin Kula da Iyakoki na zamani bisa doka”. In ji shi.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Ba Za Mu Yi Kasa A Guiwa Wajen Tabbatar Da Ingantaccen Aiki Ga Al’umma Ba – Shugaban NIS

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.