• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Taurarin Da Muke Gani A Sama Na Raguwa Duk Shekara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Yawan Taurarin Da Muke Gani A Sama Na Raguwa Duk Shekara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawan taurarin da mutane ke gani da idanunsu yana raguwa a hankali cikin shekara 10 da ta gabata.

Wannan kuwa ya faru ne sakamakon hasken da ke mamaye samaniya na fitilun da muke kunnawa a duniya – kuma tun 2011 hasken da ake samu na fitilu a duniya ke karuwa a kowacce shekara.

Dakta Christopher Kyba, wani masanin kimiyya ne a cibiyar bincike kan duniya ta Potsdam da ke Jamus, ya shaida wa BBC cewa: ” Taurarin da muke gani na raguwa”.
Shi da abokan aikinsa sun wallafa wannan bincike a jaridarsu ta kimiyya.

Wannan shi ne karshen binciken wasu masu koyon nazarin ilimin taurari da masana kimiyya na tsawon shekara 12, wadanda suke fita da daddare suna kirga taurarin da ke sama.

Rahoton da mutanen suka kammala na intanet da ake kira Globe at Night, ya mayar da hankali kan sauyin da ake samu na ganin taurari a samaniya – kuma ya yi daidai da karin kashi 10 cikin 100 da ake samu na hasken duniya a kowacce shekara.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

Wannan na nufin, yaron da aka haifa a yankin da ake iya ganin taurari 250 a sama, akwai yiwuwar nan da shekara 18 ba zai iya ganin ko taurari 100 ba a yankin.

Tiririn gurbatacciyar hasken duniya
Idan aka yi nazari kan bayanin da masu binciken nan Fabio Falchi da Salbador Bará, suka wallafa a jarida game da tiririn hasken duniya sun ce : “idan muka duba bidiyon da hukumar sararin samaniya take nunawa da kuma hotuna na duniyarmu da daddare, “Kyan hasken birane ne ke rudar mutane”, kai ka ce hasken bishiyar Kirsimeti ne.
“Ba su gane illar da ke cikin hoton ta gurbatar da hasken ke samarwa ba.
Kawai sun fi mayar da hankali ne kan kyan hoton da nau’in kalolin da suke da shi irin wanda ake gani a cikin ruwa, ba su lura da cewa tiririn gurbatattun sinadarai ne da ke tattare a cikin hasken wutar ba.
“Dakta Kyba, ya ce yana fatan ganin an samu ci gaba ta fuskar gurbatar da haske yake samar wa a ‘yan shekarun nan, saboda yawancin manyan birane suna sauya tsarin hasken da suke amfani da shi zuwa na makamashin da ba ya gurbata muhalli.
Garuruwa da birane musamman a kasashen da suka ci gaba, suna sauya fitilun kan titi zuwa masu aiki da hasken rana.
“Fatan shi ne idan za a yi amfani da wutar da ta dace, yanayin zai habaka ya yi kyau,” in ji shi.
Amma da wadannan fitilun da muke aiki da su – da yiwuwar mu sake gurbata hasken samaniyar da muke da shi.
Hukumar ta yi bayanin cewa “Cin karon da ake samu na hasken” da ake samu, ya sanya aka bullo da hasken da ake kira LED da alkawarin zai rage yawan amfani da makamashi, sannan kuma ya kara karfin gani ga bil’adama da daddare, amma hasken karuwa ma yake.
Idan aka samu cin karon da aka samu, shi ne a alkawarin sauki da kuma inganta kyau da zai yi, musamman ga al’umar da suka saba da hasken wuta.”Yawan hasken da ake samu shi ba iya illar rage taurari ya tsaya ba. Yana illa ga lafiyar dan ‘Adam da kuma tsarin yadda yake barci.
Yana haifar da matsala ga yanayin halayyar dabbobin da ba sa bacci da daddare, wanda a bayan nan wani bincike ya nuna ana samun raguwar kwari.
Shi tiririn hasken asara ce ga makamashi. Kuma kullum ci gaba muke da haska makamashi cikin sammai, wanda hakan ba daidai ba ne, in ji Daktan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Firayin Ministan Thailand: Sake Fara Ziyarar Sinawa Masu Yawon Shakatawa A Thailand Na Da Babbar Ma’ana

Next Post

Abin Da Zai Sa Na Amince Da Shan Kaye A 2023 – Kwankwaso

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

4 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

5 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

6 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

7 hours ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

8 hours ago
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Abin Da Zai Sa Na Amince Da Shan Kaye A 2023 – Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

July 4, 2025
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

July 4, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

July 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.