• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Man U Ta Maye Gurbin Eriksen Da Zai Yi Jinyar Watanni Uku

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Eriksen

Dan wasan tsakiyar kungiyar kwallon kafa ta Manchester United Christian Eriksen zai shafe akalla wata biyu yana jinya, bayan samun rauni a wasan kofin kalubale da suka buga da Reading ranar Asabar.

Sai dai kociyan kungiyar, Erik Ten Hag ya yi amanna cewa Manchester United na da ”yan wasa da za su iya cike gibin da Eriksen zai bari wanda hakan ya sa yake ganin ba shi da damuwa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Jihar Gombe Ya Koma APC Bayan Ganawarsa da Gwamna Inuwa

Ten Hag ya ce ranar karshe abu ne mai wahala a iya cike madadin dan wasa kuma a matsayinka na mai koyarwa ba za ka dauki mataki ba bagatatan saboda rauni, to amma kuma suna da ‘yan wasa a tsakiya kuma suna da kyau.

Dan wasan na Denmark ya buga wa Manchester United wasanni 31 a wannan kaka, bayan da ya rattaba hannu kan yarjejeniyar shekara uku kuma yana daya daga cikin ‘yan wasan da United take takama da su.

Kafin zuwan Eriksen Manchester United, ya yi kwallo a kungiyoyin Ajad da Tottenham da Inter Milan kafin ya tafi Brentford inda ya buga wasa a watanni shida kacal a kungiyar.
Watakila dan wasan tsakiyar ya iya kai wa har farkon watan Mayu kafin ya murmure, wato dab da a kare wannan kaka kenan kuma daman dan wasan kungiyar na tsakiya Donny Ban de Beek yana jiyya wanda ba zai dawo ba har sai bayan kammala wannan kaka.

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Sai dai kuma Manchester United din ta karbi aron dan wasa Marcel Sabitzer daga kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich wanda zai zauna har zuwa karshen wannan kakar.

Dan wasan tsakiyar na Austria mai shekaru 28 zai maye gurbin Christian Eriksen ne da ke fama da doguwar jinya da kuma Scott Mc Tominay da shima ya samu rauni a baya-bayan nan.

Sabitzer wanda Munich ta sayo daga RB Leipzig lokacin ya na matsayin kyaftin wasanni 54 ya dokawa kungiyar ta Bundesliga daga sayensa a 2021 zuwa yanzu kuma a jawabinsa bayan rattaba hannu kan yarejejeniyar zaman aron a tawagar Eric ten hag, Sabitzer ya ce amsa tayin zuwa Old Trafford matsayin aro ne saboda ya san cikakkiyar dama ce gareshi ya bayar da gudunmawarsa ga gungiyar.

A tsawon lokacin da ya shafe yana buga wasa a turai Sabitner ya buga wasanni sau 443 a filayen wasa ya yinda a bangare guda ya buga wa kasar sa wasanni 68 tare da cin kwallaye 12.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Wasanni

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
Next Post
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa'adin Karbar Tsofaffin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.