• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar-kasar Turkiyya Da Siriya Ta Jefa Duniya Cikin Alhini

by Bello Hamza
3 years ago
Girgizar-kasar Turkiyya da Siriya

Yanayin girgizar-kasa mai karfin gaske da ta auku a kasashen Turkiyya da Siriya ya jefa duniya cikin alhini sakamakon dubban mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, ya zuwa ranar laraba an tabbatar da mutuwar mutum 7,000.

Rabon a ga girgizar-kasa mai barna irin wannan a duniya tun a shekarar 1999 lokacin da kimanin mutum dubu 17 suka rasa rayukansu.

  • Girgizar Kasa: Adadin Wadanda Suka Mutu A Turkiyya Da Siriya Sun Haura 23,000

Bayan aukuwar lamarin dai, masu aikin ceto sun dukufa fafutikar ganin ko za a samo wasu da ransu a karkashin baraguzan gine-ginen da suka rufta a wasu yankunan kasashen Turkiyya da Siriya.

Sai dai ruwan sama mai karfi da dusar kankara wadda ke zuba sun rika kawo cikas ga aikin a kudu maso gabashin Turkiyya.
Shafin Hausa na BBC ya ruwaito Hukumar Lafiya ta Duniya na gargadin cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka rasa ransu a lamarin zai yi matukar karuwa.

Mutane da dama a yankunan da lamarin ya faru na jin tsoron komawa cikin gine-gine da suka rage.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Masu nazari kan motsin kasa sun ce girgizar ita ce mafi girma da aka taba samu a Turkiyya.

Al’ummar yankin sun ce an kwashe minti biyu kasa na jijjiga kafin lamarin ya dakata.
Alkaluma daga Turkiyya da Siriya na nuna cewa kawo yanzu mutum fiye da dubu biyar ne suka mutu sannan fiye da dubu 15 suka jikkata sakamakon ibtila’in girgizar kasar.

Shugabanni kasashen duniya sun yi alkawarin aikewa da tawagar ma’aikata da kayan aikin ceto ya zuwa Turkiyya don agazawa.

Rahotanni na cewa an kara samun girgizar kasa karo na biyu cikin kwana guda a kudu-maso-gabashin Turkiyya.

Hukumar lura da yanayin kasa ta Amurka ta ce karfin girgizar kasar ya kai 7.5 a kan ma’auni.

Lamarin ya faru ne a gundumar Elbistan na lardin Kahramanmaras.
Wani jami’in Hukumar Lura da Bala’o’i na Turkiyya ya tabbatar da cewa “wannan wata sabuwar girgizar kasa ce ba ragowar wadda ta faru ne a farko ba.”

Wani faifan bidiyo ya nuna yadda mutane ke gudu cikin rudewa a lokacin da girgizar ta biyu ta faru.

An ga mutanen suna ihu, suna gudu a kan tituna a lokacin da kura ke lafawa bayan gine-gine sun rufta.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta afka wa yankin Gaziantep da ke kudancin Turkiyya a tsakiyar daren Litinin.

Kuma an jiyo ruguginta har a yankin Gaza. An kuma samu rushewar gidaje a Lebanon.
Turkiyya dai ta ayyana dokar ta baci tare da kira ga mutane su dakatar da amfani da wayoyinsu, saboda masu aikin agaji su samu damar kai wa ga wadanda suka makale a cikin baraguzai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.