• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu

by Umar Faruk
3 years ago
Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga durkushewa.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake jawabi a taron yakin neman zabensa a Birnin Kebbi na Jihar Kebbi.

  • Emmanuel Bwacha Ya Lashe Zaben Fidda Gwanin APC A Taraba
  • Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

Ya ce, sana’ar kifi a Jihar Kebbi za ta hade da Legas ta yadda zai bunkasa tattalin arzikin jihar tare da samar da karin guraben ayyukan yi ga dimbin matasan jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zai warware matsalar rashin tsaro da karancin mai a jihar.

Dan takarar, ya nuna jin dadinsa kan yadda dimbin magoya baya suka tarbe shi a jihar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Ya jinjina wa Gwamna Jihar, Atiku Bagudu da shugabannin jam’iyyar APC na jihar da kuma duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin samun nasarar yakin neman zabensa a jihar.

A nasa jawabin, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya bayyana dimbin jama’ar da suka hallara a wurin taron a matsayin shaida ne na kyakkyawan shugabancin Bagudu a jihar.

A cewarsa, “Mun gamsu da fitowar da muka gani a nan filin wasa na Haliru Audu domin yakin neman zaben shugaban kasa. Wannan shaida ce cewar Jihar Kebbi gidan APC ne. Muna godiya ga jama’a da gwamnatin jihar bisa kokarin da suke yi na ganin taron yakin neman zaben shugaban kasa a Birnin Kebbi ya zama kasance cikin nasara.

“Ina kira gare ku, a yayin da kuke taron gangamin nuna goyon baya ga dan takararmu na shugaban kasa a yau da sauran ‘yan takara, da ku sake fitowa ranar 25 ga watan Fabrairu tare da katin zabenku ku zabi dukkan ‘yan takarar APC, domin Asiwaju Bola Ahmed ya samu nasara,” in ji shi.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, a jawabinsa ya ce, dandazon jama’ar da suka fito wajen taron wata alama ce cewa APC za ta lashe zabe a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma yi godiya da goyon bayan da kowa ya ba shi “Ina yi wa dan takarar shugaban kasa da mukarrabansa fatan komawa Abuja lafiya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato
Manyan Labarai

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 
Labarai

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Next Post
Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.