• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga durkushewa.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake jawabi a taron yakin neman zabensa a Birnin Kebbi na Jihar Kebbi.

  • Emmanuel Bwacha Ya Lashe Zaben Fidda Gwanin APC A Taraba
  • Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

Ya ce, sana’ar kifi a Jihar Kebbi za ta hade da Legas ta yadda zai bunkasa tattalin arzikin jihar tare da samar da karin guraben ayyukan yi ga dimbin matasan jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zai warware matsalar rashin tsaro da karancin mai a jihar.

Dan takarar, ya nuna jin dadinsa kan yadda dimbin magoya baya suka tarbe shi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Ya jinjina wa Gwamna Jihar, Atiku Bagudu da shugabannin jam’iyyar APC na jihar da kuma duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin samun nasarar yakin neman zabensa a jihar.

A nasa jawabin, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya bayyana dimbin jama’ar da suka hallara a wurin taron a matsayin shaida ne na kyakkyawan shugabancin Bagudu a jihar.

A cewarsa, “Mun gamsu da fitowar da muka gani a nan filin wasa na Haliru Audu domin yakin neman zaben shugaban kasa. Wannan shaida ce cewar Jihar Kebbi gidan APC ne. Muna godiya ga jama’a da gwamnatin jihar bisa kokarin da suke yi na ganin taron yakin neman zaben shugaban kasa a Birnin Kebbi ya zama kasance cikin nasara.

“Ina kira gare ku, a yayin da kuke taron gangamin nuna goyon baya ga dan takararmu na shugaban kasa a yau da sauran ‘yan takara, da ku sake fitowa ranar 25 ga watan Fabrairu tare da katin zabenku ku zabi dukkan ‘yan takarar APC, domin Asiwaju Bola Ahmed ya samu nasara,” in ji shi.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, a jawabinsa ya ce, dandazon jama’ar da suka fito wajen taron wata alama ce cewa APC za ta lashe zabe a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma yi godiya da goyon bayan da kowa ya ba shi “Ina yi wa dan takarar shugaban kasa da mukarrabansa fatan komawa Abuja lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtiku BaguduJihar KebbiTinubuYakin Neman Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Gaggauta Tura Ma’aikatan Ceto Zuwa Turkiye Da Syria Da Girgizar Kasa Ta Aukawa

Next Post

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

47 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.