• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Zan Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga durkushewa.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake jawabi a taron yakin neman zabensa a Birnin Kebbi na Jihar Kebbi.

  • Emmanuel Bwacha Ya Lashe Zaben Fidda Gwanin APC A Taraba
  • Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

Ya ce, sana’ar kifi a Jihar Kebbi za ta hade da Legas ta yadda zai bunkasa tattalin arzikin jihar tare da samar da karin guraben ayyukan yi ga dimbin matasan jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zai warware matsalar rashin tsaro da karancin mai a jihar.

Dan takarar, ya nuna jin dadinsa kan yadda dimbin magoya baya suka tarbe shi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ya jinjina wa Gwamna Jihar, Atiku Bagudu da shugabannin jam’iyyar APC na jihar da kuma duk wadanda suka bayar da gudunmawa domin samun nasarar yakin neman zabensa a jihar.

A nasa jawabin, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya bayyana dimbin jama’ar da suka hallara a wurin taron a matsayin shaida ne na kyakkyawan shugabancin Bagudu a jihar.

A cewarsa, “Mun gamsu da fitowar da muka gani a nan filin wasa na Haliru Audu domin yakin neman zaben shugaban kasa. Wannan shaida ce cewar Jihar Kebbi gidan APC ne. Muna godiya ga jama’a da gwamnatin jihar bisa kokarin da suke yi na ganin taron yakin neman zaben shugaban kasa a Birnin Kebbi ya zama kasance cikin nasara.

“Ina kira gare ku, a yayin da kuke taron gangamin nuna goyon baya ga dan takararmu na shugaban kasa a yau da sauran ‘yan takara, da ku sake fitowa ranar 25 ga watan Fabrairu tare da katin zabenku ku zabi dukkan ‘yan takarar APC, domin Asiwaju Bola Ahmed ya samu nasara,” in ji shi.

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, a jawabinsa ya ce, dandazon jama’ar da suka fito wajen taron wata alama ce cewa APC za ta lashe zabe a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kuma yi godiya da goyon bayan da kowa ya ba shi “Ina yi wa dan takarar shugaban kasa da mukarrabansa fatan komawa Abuja lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtiku BaguduJihar KebbiTinubuYakin Neman Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Gaggauta Tura Ma’aikatan Ceto Zuwa Turkiye Da Syria Da Girgizar Kasa Ta Aukawa

Next Post

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

1 hour ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

2 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

2 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

3 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

6 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

6 hours ago
Next Post
Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.