ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

by Sulaiman
3 years ago
Farfesa Yakubu

Daidai saura makonni biyu a gudanar da zaɓe, Shugaban Hukumar Zaɓe na Ƙasa Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar wa Shugabannin Jami’o’i cewa za a kare rayuka da lafiyar dukkan malaman da za su yi aikin zaɓe.

 

Yakubu ya ce INEC na aiki tare da dukkan ɓangarorin jami’an tsaro na faɗin ƙasar nan domin samar da cikakken tsaro ga ma’aikatan da za su yi aikin zaɓe a matakai daban-daban har matakai 10.

ADVERTISEMENT
  • CBN Ya Tabbatarwa INEC Samun Wadatattun Takardun Naira Don Gudanar Da Zaben 2023

Daga saman jerin sunayen muƙaman masu aikin zaɓe akwai Babban Baturen Zaɓe na Jiha, Jami’an Tattara Sakamakon Zaɓe na Jihohi, Baturen Zaɓe da Mataimakin sa da kuma masu sa-idon da aka tantance yardar su kula da yadda ake gudanar da zaɓen. Akwai kuma ‘yan jarida, waɗanda su ma waɗanda aka tantance ne za su riƙa zagayawa ɗauko labaran abin da ke faruwa a rumfunan zaɓe da cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen.

 

LABARAI MASU NASABA

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

Shugaban INEC ya ce an tanadi inshora ga duk wani ma’aikacin da aka tantance zai yi aikin zaɓe.

 

Shugabannin jami’o’i sun nuna wa Shugaban INEC abubuwan da su ke da damuwa a kai, a lokacin ganawar ta su a Hedikwatar Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa, wadda ke kusa da Hedikwatar INEC a Abuja, a ranar Alhamis.

Farfesa Yakubu

Yakubu ne dai ya nemi a yi ganawar domin nan amincewa a ɗauki sunayen malaman jami’o’i da za su yi aikin zaɓe.

 

Sai dai wasu shugabannin jami’o’in sun nuna ɗar-ɗar dangane da matsalar tsaro a wasu yankunan da za a tura wasu malaman a wuraren da ba cikin birane ba.

 

A nan, Yakubu ya tabbatar masu da cewa a ko’ina har a cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.

 

Ya ce ya gana da shugabannin ɓangarorin tsaro na ƙasar nan, kuma sun tabbatar masa da cewa za su samar da isasshen tsaro.

Farfesa Yakubu

“Za mu yi aiki ne tare da ma’aikatan tsaro, kuma sun tabbatar min cewa za su samar da isasshen tsaro.

 

Yakubu ya ce za a fara horas da malaman jami’o’i aikin zaɓe a ranakun 21 da 22 ga Fabrairu.

Farfesa Yakubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Farfesa Yakubu
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
Labarai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Next Post
Wani Ya Rasu Yayin Da Magoya Bayan APC Da PDP Suka Yi Arangama Da Juna A Jigawa

Wani Ya Rasu Yayin Da Magoya Bayan APC Da PDP Suka Yi Arangama Da Juna A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Farfesa Yakubu

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Farfesa Yakubu

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.