• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Bai Wa Gombawa Kunya Ba – Inuwa Yahaya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya kuma dan takarar Gwamnan Jihar Gombe, ya ayyana cewar, shi kam yana alfahari da cewa bai baiwa al’ummar jiharsa kunya ba domin ya zage damtse ya gudanar da ayyukan raya jihar da har ake alfahari da shi. 

 

Ya ce, ayyukan da ya shimfida su ne za su zama masa asasi wajen sake zama gwamna a zaben 2023 da ke tafe.

  • Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Inuwa ya shaida hakan ne a lokacin da ke jawabi yayin kaddamar da yakin zaben Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da aka gudanar a ranar Litinin a Jihar, ya kara da cewa al’ummar Gombe sun Yi alkawarin za su zabi Tinubu a matsayin shugaban kasa, da shi a matsayin gwamna hadi da sauran ‘yan takara.

 

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Muhammadu ya ce ko yanzu aka ja layin zaben a jihar ya tabbatar zai ci zabensa babu hamayya domin Gwambawa su na tare da shi.

 

A kan hakan ya shelanta wa al’ummar jihar cewa Idan suka zabi Tinubu a matsayin shugaban kasa zai daura daga inda Buhari ya tsaya domin kara nausa kasar nan zuwa mataki na gaba.

 

Ya yi amfani da wannan damar wajen gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa muhimman ayyukan da ya aiwatar a jihar da ma Arewa Maso Gabas baki daya.

 

Daga nan sai ya roki al’ummar jihar da su zabi APC a dukkanin matakai.

 

A nasa jawabin, mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Alhaji Kasim Shettima, ya tabbatar wa al’ummar Gombe cewa APC za ta rike amana kuma za ta yi kokarinta wajen shawo kan matsalolin da suke akwai muddin aka sake ba ta dama.

 

Ya yi shelanta wa al’ummar arewa Maso Gabas cewa muddin suna son aikin halo Mai da aka samu a Gombe da Bauchi ya tabbatar, to su amince su sake zabin APC domin su ne suka san yadda za su yi a fara lasar albarkatun Mai din.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Inuwa
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
Next Post
Takarar Musulmai 2: Asiwaju Ya Gana Da Shugabannin CAN,  “Kiristoci ‘Ya’yana Ne” —Tinubu

Gwamnatina Za Ta Tabbatar An Fara Hako Mai A Bauchi Da Gombe - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Inuwa

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.