ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Za Mu Zabi Atiku Abubakar Ba Tare Da Sharadi Ba - Gwamna Bala

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya sha alwashin cewa, a matsayinsa na dan Arewa Maso Gabas mai kuma kishin yankin zai tabbatar an dauki dukkanin matakan da suka dace wajen ganin an fara fito da arzikin Mai da Allah ya albarkaci jihohin Bauchi da Gombe da su muddin aka zabeshi a matsayin shugaban kasa a 2023. 

 

A cewarsa, “Shekara da shekaru ana cewa akwai Mai a Arewa Maso Gabas daga Nijar, yanzu an dawo Bauchi da Gombe, yau ga naku dan Arewa Maso Gabas. Idan kun zabi PDP za mu tabbatar da aikin Man nan an yi shi wannan karon, ba za a rufe mana rijiya a ce a’a ba na Mai ba. Ina son na muku wannan alkawarin insha Allah.”

ADVERTISEMENT
  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Atiku wanda ke wannan bayanin a ranar Talata a jihar Bauchi yayin kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 a jihar Bauchi da ya samu halartar dubban jama’a, kana kusoshin jam’iyyar da dama sun halarci gangamin da ya gudana a dandalin wasanni ta Sitadiyum da ke jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Ya kara da cewa, “Mutane su na tambaya wai shin in an debo Mai din nan ta yaya za a fitar da ita, ina son na fada muku cewa za mu farfado da hanyar Jirgin kasa wanda za mu yi amfani da shi ya dibi Mai din nan zuwa inda duk za a kai.”

 

“Ai ga Nijar su na hakar Mai ko ba su yi ne? Ba su fitar da Mai din? Ai ga Chadi su na hakar Mai, ba su fitar da Mai din ne? To muma muna da hanyoyin da za mu fitar da Mai dinmu insha Allah.”

 

Atiku ya kara da daukan alkawarin cewa, zai samar da tallafin sana’o’in dogaro da kai ga mata da matasa wanda a cewarsa idan ya zama shugaban kasa zai ware maguden kudade da za a raba ga al’umma a matsayin tallafin sana’o’in dogaro da kai domin fitar da jama’a daga cikin kangin talauci da fatara.

 

“Za mu fitar da maguden kudade masu yawa da za mu bai wa masu yin sana’a mata da Matasa musamman matasa domin a rage matsalar zaman banza. Don haka ba ku da wata jam’iyya kamar jam’iyyar PDP.”

 

Ya roki jama’a da su zabi PDP a dukkanin matakai, ya kuma gode kan yadda jama’a suka fito domin nuna masa soyayya da kauna.

 

Atiku ya ce kusan watanni biyu su na yawon zaga Nijeriya domin yakin zabe amma ba su ga inda aka Allah ya nuna musu yawan mutane kamar jihar Bauchi ba, don haka ya nuna hakan a matsayin karamci sosai da aka masa kuma ya misalta hakan a matsayin alamun nasara.

 

“Wadanda suke karya suke cewa gwamna Bala Muhammad bai gina PDP a Bauchi ba yau mun zo mun ga yadda Kaura ya gina PDP a Bauchi. Don haka Bauchi sai Bala.

 

“Bari na gaya muku, kuma ina rokonku duk wani wanda zai zabeni a jihar Bauchi, kai dan PDP ne, kai dan APC ne, kai dan Labour ne, ko kai dan kowace jam’iyya ne, in ka zabeni to ka zabi Kaura.

 

“Wannan shi ne mutanen APC a da suka zo su na ce mana sak, to yanzu muma za mu ce musu PDP sak, PDP sak daga sama zuwa kasa.”

 

Shi kuma a nasa jawabin, gwaman jihar Bauchi, Bala Muhammad ya shaida cewar za su fito su zabi Atiku Abubakar ba tare da wani sharadi ba domin sun tabbatar zai ceto Nijeriya daga halin da take ciki.

 

A cewar Bala Muhammad, “Kai mai gidanmu ne Babanmu ne, ba za mu baka wasu roke-roke ba sai mun kauce za mu gaya maka abubuwan da suka damemu, amma wadannan din ma ba sharadi ba ne. Za mu zabeka ba tare da wani sharadi ba, za mu zabeka ba sai ka bamu komai ba domin kai ne mu, mu ne kai.

 

“A matsayina na gwamnan Jihar Bauchi ina maka godiya da ka nuna dattako, sauran mutane ma da suka nuna tababa muna rokonka ka gaya musu su su yi biyayya wa nau’in mulki da PDP saboda mu zauna mu ci zabe ba tare da wani hamayya ba.”

 

Ya bai wa Atiku tabbacin cewa jama’a za su zabe shi a jihar, “Mai girma Wazirin Adamawa Bauchi taka ce, Bauchi ta PDP ne, kuma ba mu da wata miskila. Akwai wasu masu karya su na nuna banbance-banbance a nau’in shugabanci, za mu yi hakuri da su saboda shure-shure baya hana mutuwa.

 

“Wannan jiha ko ka zo ko baka zo ba, ina tabbatar maka za ka ci zabe a Bauchi fiye da kowace jiha a Nijeriya.”

 

Ya yi amfani da wannan damar wajen gode wa dandazon wadanda suka sauya sheka daga wasu Jam’iyyu zuwa PDP a jihar, ya nuna hakan da cewa ya kara musu tabbacin samun nasara a zaben da ke tafe.

Atiku
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Atiku
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.