ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Za Mu Zabi Atiku Abubakar Ba Tare Da Sharadi Ba - Gwamna Bala

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya sha alwashin cewa, a matsayinsa na dan Arewa Maso Gabas mai kuma kishin yankin zai tabbatar an dauki dukkanin matakan da suka dace wajen ganin an fara fito da arzikin Mai da Allah ya albarkaci jihohin Bauchi da Gombe da su muddin aka zabeshi a matsayin shugaban kasa a 2023. 

 

A cewarsa, “Shekara da shekaru ana cewa akwai Mai a Arewa Maso Gabas daga Nijar, yanzu an dawo Bauchi da Gombe, yau ga naku dan Arewa Maso Gabas. Idan kun zabi PDP za mu tabbatar da aikin Man nan an yi shi wannan karon, ba za a rufe mana rijiya a ce a’a ba na Mai ba. Ina son na muku wannan alkawarin insha Allah.”

ADVERTISEMENT
  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Atiku wanda ke wannan bayanin a ranar Talata a jihar Bauchi yayin kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 a jihar Bauchi da ya samu halartar dubban jama’a, kana kusoshin jam’iyyar da dama sun halarci gangamin da ya gudana a dandalin wasanni ta Sitadiyum da ke jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Ya kara da cewa, “Mutane su na tambaya wai shin in an debo Mai din nan ta yaya za a fitar da ita, ina son na fada muku cewa za mu farfado da hanyar Jirgin kasa wanda za mu yi amfani da shi ya dibi Mai din nan zuwa inda duk za a kai.”

 

“Ai ga Nijar su na hakar Mai ko ba su yi ne? Ba su fitar da Mai din? Ai ga Chadi su na hakar Mai, ba su fitar da Mai din ne? To muma muna da hanyoyin da za mu fitar da Mai dinmu insha Allah.”

 

Atiku ya kara da daukan alkawarin cewa, zai samar da tallafin sana’o’in dogaro da kai ga mata da matasa wanda a cewarsa idan ya zama shugaban kasa zai ware maguden kudade da za a raba ga al’umma a matsayin tallafin sana’o’in dogaro da kai domin fitar da jama’a daga cikin kangin talauci da fatara.

 

“Za mu fitar da maguden kudade masu yawa da za mu bai wa masu yin sana’a mata da Matasa musamman matasa domin a rage matsalar zaman banza. Don haka ba ku da wata jam’iyya kamar jam’iyyar PDP.”

 

Ya roki jama’a da su zabi PDP a dukkanin matakai, ya kuma gode kan yadda jama’a suka fito domin nuna masa soyayya da kauna.

 

Atiku ya ce kusan watanni biyu su na yawon zaga Nijeriya domin yakin zabe amma ba su ga inda aka Allah ya nuna musu yawan mutane kamar jihar Bauchi ba, don haka ya nuna hakan a matsayin karamci sosai da aka masa kuma ya misalta hakan a matsayin alamun nasara.

 

“Wadanda suke karya suke cewa gwamna Bala Muhammad bai gina PDP a Bauchi ba yau mun zo mun ga yadda Kaura ya gina PDP a Bauchi. Don haka Bauchi sai Bala.

 

“Bari na gaya muku, kuma ina rokonku duk wani wanda zai zabeni a jihar Bauchi, kai dan PDP ne, kai dan APC ne, kai dan Labour ne, ko kai dan kowace jam’iyya ne, in ka zabeni to ka zabi Kaura.

 

“Wannan shi ne mutanen APC a da suka zo su na ce mana sak, to yanzu muma za mu ce musu PDP sak, PDP sak daga sama zuwa kasa.”

 

Shi kuma a nasa jawabin, gwaman jihar Bauchi, Bala Muhammad ya shaida cewar za su fito su zabi Atiku Abubakar ba tare da wani sharadi ba domin sun tabbatar zai ceto Nijeriya daga halin da take ciki.

 

A cewar Bala Muhammad, “Kai mai gidanmu ne Babanmu ne, ba za mu baka wasu roke-roke ba sai mun kauce za mu gaya maka abubuwan da suka damemu, amma wadannan din ma ba sharadi ba ne. Za mu zabeka ba tare da wani sharadi ba, za mu zabeka ba sai ka bamu komai ba domin kai ne mu, mu ne kai.

 

“A matsayina na gwamnan Jihar Bauchi ina maka godiya da ka nuna dattako, sauran mutane ma da suka nuna tababa muna rokonka ka gaya musu su su yi biyayya wa nau’in mulki da PDP saboda mu zauna mu ci zabe ba tare da wani hamayya ba.”

 

Ya bai wa Atiku tabbacin cewa jama’a za su zabe shi a jihar, “Mai girma Wazirin Adamawa Bauchi taka ce, Bauchi ta PDP ne, kuma ba mu da wata miskila. Akwai wasu masu karya su na nuna banbance-banbance a nau’in shugabanci, za mu yi hakuri da su saboda shure-shure baya hana mutuwa.

 

“Wannan jiha ko ka zo ko baka zo ba, ina tabbatar maka za ka ci zabe a Bauchi fiye da kowace jiha a Nijeriya.”

 

Ya yi amfani da wannan damar wajen gode wa dandazon wadanda suka sauya sheka daga wasu Jam’iyyu zuwa PDP a jihar, ya nuna hakan da cewa ya kara musu tabbacin samun nasara a zaben da ke tafe.

Atiku
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.