ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Za Mu Zabi Atiku Abubakar Ba Tare Da Sharadi Ba - Gwamna Bala

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya sha alwashin cewa, a matsayinsa na dan Arewa Maso Gabas mai kuma kishin yankin zai tabbatar an dauki dukkanin matakan da suka dace wajen ganin an fara fito da arzikin Mai da Allah ya albarkaci jihohin Bauchi da Gombe da su muddin aka zabeshi a matsayin shugaban kasa a 2023. 

 

A cewarsa, “Shekara da shekaru ana cewa akwai Mai a Arewa Maso Gabas daga Nijar, yanzu an dawo Bauchi da Gombe, yau ga naku dan Arewa Maso Gabas. Idan kun zabi PDP za mu tabbatar da aikin Man nan an yi shi wannan karon, ba za a rufe mana rijiya a ce a’a ba na Mai ba. Ina son na muku wannan alkawarin insha Allah.”

ADVERTISEMENT
  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Atiku wanda ke wannan bayanin a ranar Talata a jihar Bauchi yayin kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 a jihar Bauchi da ya samu halartar dubban jama’a, kana kusoshin jam’iyyar da dama sun halarci gangamin da ya gudana a dandalin wasanni ta Sitadiyum da ke jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Ya kara da cewa, “Mutane su na tambaya wai shin in an debo Mai din nan ta yaya za a fitar da ita, ina son na fada muku cewa za mu farfado da hanyar Jirgin kasa wanda za mu yi amfani da shi ya dibi Mai din nan zuwa inda duk za a kai.”

 

“Ai ga Nijar su na hakar Mai ko ba su yi ne? Ba su fitar da Mai din? Ai ga Chadi su na hakar Mai, ba su fitar da Mai din ne? To muma muna da hanyoyin da za mu fitar da Mai dinmu insha Allah.”

 

Atiku ya kara da daukan alkawarin cewa, zai samar da tallafin sana’o’in dogaro da kai ga mata da matasa wanda a cewarsa idan ya zama shugaban kasa zai ware maguden kudade da za a raba ga al’umma a matsayin tallafin sana’o’in dogaro da kai domin fitar da jama’a daga cikin kangin talauci da fatara.

 

“Za mu fitar da maguden kudade masu yawa da za mu bai wa masu yin sana’a mata da Matasa musamman matasa domin a rage matsalar zaman banza. Don haka ba ku da wata jam’iyya kamar jam’iyyar PDP.”

 

Ya roki jama’a da su zabi PDP a dukkanin matakai, ya kuma gode kan yadda jama’a suka fito domin nuna masa soyayya da kauna.

 

Atiku ya ce kusan watanni biyu su na yawon zaga Nijeriya domin yakin zabe amma ba su ga inda aka Allah ya nuna musu yawan mutane kamar jihar Bauchi ba, don haka ya nuna hakan a matsayin karamci sosai da aka masa kuma ya misalta hakan a matsayin alamun nasara.

 

“Wadanda suke karya suke cewa gwamna Bala Muhammad bai gina PDP a Bauchi ba yau mun zo mun ga yadda Kaura ya gina PDP a Bauchi. Don haka Bauchi sai Bala.

 

“Bari na gaya muku, kuma ina rokonku duk wani wanda zai zabeni a jihar Bauchi, kai dan PDP ne, kai dan APC ne, kai dan Labour ne, ko kai dan kowace jam’iyya ne, in ka zabeni to ka zabi Kaura.

 

“Wannan shi ne mutanen APC a da suka zo su na ce mana sak, to yanzu muma za mu ce musu PDP sak, PDP sak daga sama zuwa kasa.”

 

Shi kuma a nasa jawabin, gwaman jihar Bauchi, Bala Muhammad ya shaida cewar za su fito su zabi Atiku Abubakar ba tare da wani sharadi ba domin sun tabbatar zai ceto Nijeriya daga halin da take ciki.

 

A cewar Bala Muhammad, “Kai mai gidanmu ne Babanmu ne, ba za mu baka wasu roke-roke ba sai mun kauce za mu gaya maka abubuwan da suka damemu, amma wadannan din ma ba sharadi ba ne. Za mu zabeka ba tare da wani sharadi ba, za mu zabeka ba sai ka bamu komai ba domin kai ne mu, mu ne kai.

 

“A matsayina na gwamnan Jihar Bauchi ina maka godiya da ka nuna dattako, sauran mutane ma da suka nuna tababa muna rokonka ka gaya musu su su yi biyayya wa nau’in mulki da PDP saboda mu zauna mu ci zabe ba tare da wani hamayya ba.”

 

Ya bai wa Atiku tabbacin cewa jama’a za su zabe shi a jihar, “Mai girma Wazirin Adamawa Bauchi taka ce, Bauchi ta PDP ne, kuma ba mu da wata miskila. Akwai wasu masu karya su na nuna banbance-banbance a nau’in shugabanci, za mu yi hakuri da su saboda shure-shure baya hana mutuwa.

 

“Wannan jiha ko ka zo ko baka zo ba, ina tabbatar maka za ka ci zabe a Bauchi fiye da kowace jiha a Nijeriya.”

 

Ya yi amfani da wannan damar wajen gode wa dandazon wadanda suka sauya sheka daga wasu Jam’iyyu zuwa PDP a jihar, ya nuna hakan da cewa ya kara musu tabbacin samun nasara a zaben da ke tafe.

Atiku
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.