Hadakar jami’an tsaro sojin kasa da na ruwa sun hallaka ‘yan bindiga bakwai a yayin wani samamen kakkebe ‘yan ta’adda a yankin Kasso da ke karamar hukumar Chikum a Jihar Kaduna.
A wata sanarwar manema labarai da Kwamishinan Kula da Harkokin Tsaron Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, bayanan da gwamnatin Jihar Kaduna ta samu na sakamakon aikin, ya yi nuni da cewa sojojin sun cimma ‘yan bindigae ne a wajen kauyen Ungwani Rimi da ke Kasso a kusa da wani ruwa.
- NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a
- Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba –Matasan Arewa A Kudu
Sanarwar ta ce, haduwar tasu ke da wuya sojojin sun sha karfin ‘yan bindigar a lokacin da suka gwabza fada a tsakaninsu.
Aruwan, ya kara da cewa sojojin sun kwato babura guda biyar, alburusai guda 153, da wasu alburusai guda bakwai tare da wayoyin hannu guda uku a lokacin arangamar.
“’Yan bindiga bakwai ne aka tabbatar da kashesu a yayin harin, tare da tunanin wasu ma za su iya bin sawunsu da wadanda suka jikkata a kusa da wani kogi.
“Lokacin da ya samu rahoton, gwamna Nasiru El-Rufai ya jinjina tare da yaba wa kokarin dakarun sojojin tare da fatan za su kara ninka kokarinsu domin dakile aniyar ‘yan bindiga a jihar
“Sannan, gwamnan ya kuma jinjina wa jagorancin Manjo-Janar TA Lagbaja, GOC na runduna ta daya da Cdre ME Ejumabone, kwamandan kwalejin horas da sojojin ruwa NNSAT, bisa nasarorin da suka samu,” in ji Aruwan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp