ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

by Ibrahim Bala
9 months ago
Boko

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan shafi me albarka. A wannan makon zan yi bayani wanda kacokan muka dauke shi daga kan rayuwar mu ta daidai muka mayar da shi rayuwar mu ta ba daidai ba, kuma shi ne ginshikin rayuwa ma’ana ilimi.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

Zan yi magana a kan ilimi musamman ilimin ‘ya’ya mata. Alal hakikanin gaskiya wani nazari da tunani muka yi muka gane cewar, “me ya sa yanzu muka fifita ilimin boko akan na addini, musamman ga ‘ya’ya mata?”.

ADVERTISEMENT

Annabi ya ce mu nemi ilimi ko da a burnin Sin ne, sai dai wani abun tunani da hange a wannan yanayi da muke ciki, kowane iyaye burinsu da hangensu bai wuce na, Ya za a yi ‘ya’yansu su mallaki degree, babu ruwansu da la’akari cewar ya kamata ‘ya’yansu su san alkur’ani, su san Allah ba, wanda alkur’ani ilimin addini shi ne ilimin sanin Allah da manzonsa, kuma shi ne ilimin sanin addinin Allah.

Amma me ya sa hankalinmu ya fi karkata ga ilimin boko, za ka ga idan karatun boko za a kai yaro babu matsala, komai ake bukata za a yi, amma ilimin addini ba a bashi wannan gudunmawar.

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Ita kanta gwamnatin da muke ciki za a ga rayuwar gwamnatin ta fi karkata da a taimakawa ilimin bokon, me ya sa muka yar da ilimin da Allah zai tambaye mu a kansa ranar gobe alkiyama?

Babu ruwan ubangiji da karatunka na boko, da aka ce ka je ka yi ilimi ba an ce ka je ka yi ilimin boko kadai ba, me ya sa muka fifita ilimin boko akan na addini?

Kowa ya fi ganin burgewa a kan ‘ya’yansa su iya turanci akan larabci, kullum idan ka yi magana sai a ce zamani ne ya zo da shi. Idan da za mu bawa kur’ani da addini mahimmanci fiye da ilimin boko wallahi tallahi akwai matsalolin da ba za mu shiga ba. Wannan mace-macen auren da suke yawa wallahi da ba su mutu ba, saboda wani lokacin a ilimin addini za ka samu mace ko namiji ya san ya ake aure, ya ake zaman aure, ya hakkin aure yake. Amma boko sai a ce ‘yan boko ne, da makamancin haka.

Ya kamata mu farga za a wayi gari lokacin da za a ga babu ma masu ilimin addinin da karfi ‘especially’ mata da ake yi wa aure, tunda burin kowa ne kawai ‘yar sa ta yi jami’a ta yi boko, ta samu ‘degree’, ta samu ‘masters’, ta zama abubuwa da yawa gashi nan dai. Sai ka ga rayuwar kawai tana tabarbarewa ana ta barin Allah, ana ta barin addinin Allah, ana ta barin hanyoyi na daidai, sai ace, ai ‘yan boko ne.

To, ni shawara nake bayarwa ba mu ce kar a yi karatun boko ba tunda zamani ne ya zo da shi, kuma shi ma ilimi ne. Amma ya zamanto iyaye da masu dama an yi fifti-fifti a bawa ilimin boko karfi, a bawa na addini karfi. Saboda rayuwar yanzu an tsinci kai cikin wata iriyar rayuwa ta gudun yada kanin wani akan tarbiyyar iyalai da ‘ya’ya da sauransu.

A da’ za ka ga makota ma suna iya tarbiyyar ‘ya’yan wani, amma yanzu mutum ma dakyar yake iya tarbiyyar nasa. Dan haka da ace tuntuni hanyoyin da muka bi na karatun boko haka muka bi na karatun addini, wallahi tallahi da tuni ilimin sani da tsoron Allah ya wadace mu sosai.

Allah ubangiji ya sa mu dace, Allah ubangiju ya amfanar da karatun da muka yi, ubangiji Allah ya kara buda kwakwalwar dalibanmu da mu kanmu bakidaya da sauran al’umma.

Boko
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya - Ministan Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.