ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

by Ibrahim Bala
6 months ago
Boko

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan shafi me albarka. A wannan makon zan yi bayani wanda kacokan muka dauke shi daga kan rayuwar mu ta daidai muka mayar da shi rayuwar mu ta ba daidai ba, kuma shi ne ginshikin rayuwa ma’ana ilimi.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

Zan yi magana a kan ilimi musamman ilimin ‘ya’ya mata. Alal hakikanin gaskiya wani nazari da tunani muka yi muka gane cewar, “me ya sa yanzu muka fifita ilimin boko akan na addini, musamman ga ‘ya’ya mata?”.

ADVERTISEMENT

Annabi ya ce mu nemi ilimi ko da a burnin Sin ne, sai dai wani abun tunani da hange a wannan yanayi da muke ciki, kowane iyaye burinsu da hangensu bai wuce na, Ya za a yi ‘ya’yansu su mallaki degree, babu ruwansu da la’akari cewar ya kamata ‘ya’yansu su san alkur’ani, su san Allah ba, wanda alkur’ani ilimin addini shi ne ilimin sanin Allah da manzonsa, kuma shi ne ilimin sanin addinin Allah.

Amma me ya sa hankalinmu ya fi karkata ga ilimin boko, za ka ga idan karatun boko za a kai yaro babu matsala, komai ake bukata za a yi, amma ilimin addini ba a bashi wannan gudunmawar.

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Ita kanta gwamnatin da muke ciki za a ga rayuwar gwamnatin ta fi karkata da a taimakawa ilimin bokon, me ya sa muka yar da ilimin da Allah zai tambaye mu a kansa ranar gobe alkiyama?

Babu ruwan ubangiji da karatunka na boko, da aka ce ka je ka yi ilimi ba an ce ka je ka yi ilimin boko kadai ba, me ya sa muka fifita ilimin boko akan na addini?

Kowa ya fi ganin burgewa a kan ‘ya’yansa su iya turanci akan larabci, kullum idan ka yi magana sai a ce zamani ne ya zo da shi. Idan da za mu bawa kur’ani da addini mahimmanci fiye da ilimin boko wallahi tallahi akwai matsalolin da ba za mu shiga ba. Wannan mace-macen auren da suke yawa wallahi da ba su mutu ba, saboda wani lokacin a ilimin addini za ka samu mace ko namiji ya san ya ake aure, ya ake zaman aure, ya hakkin aure yake. Amma boko sai a ce ‘yan boko ne, da makamancin haka.

Ya kamata mu farga za a wayi gari lokacin da za a ga babu ma masu ilimin addinin da karfi ‘especially’ mata da ake yi wa aure, tunda burin kowa ne kawai ‘yar sa ta yi jami’a ta yi boko, ta samu ‘degree’, ta samu ‘masters’, ta zama abubuwa da yawa gashi nan dai. Sai ka ga rayuwar kawai tana tabarbarewa ana ta barin Allah, ana ta barin addinin Allah, ana ta barin hanyoyi na daidai, sai ace, ai ‘yan boko ne.

To, ni shawara nake bayarwa ba mu ce kar a yi karatun boko ba tunda zamani ne ya zo da shi, kuma shi ma ilimi ne. Amma ya zamanto iyaye da masu dama an yi fifti-fifti a bawa ilimin boko karfi, a bawa na addini karfi. Saboda rayuwar yanzu an tsinci kai cikin wata iriyar rayuwa ta gudun yada kanin wani akan tarbiyyar iyalai da ‘ya’ya da sauransu.

A da’ za ka ga makota ma suna iya tarbiyyar ‘ya’yan wani, amma yanzu mutum ma dakyar yake iya tarbiyyar nasa. Dan haka da ace tuntuni hanyoyin da muka bi na karatun boko haka muka bi na karatun addini, wallahi tallahi da tuni ilimin sani da tsoron Allah ya wadace mu sosai.

Allah ubangiji ya sa mu dace, Allah ubangiju ya amfanar da karatun da muka yi, ubangiji Allah ya kara buda kwakwalwar dalibanmu da mu kanmu bakidaya da sauran al’umma.

Boko
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya - Ministan Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.