• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru 3 bayan barkewar annobar cutar numfashi ta COVID-19 a duniya, kasar Sin tana mayar da jama’arta da rayukansu a gaban kome. Ta kuma kyautata matakan yaki da cutar bisa lokaci da yanayin da ake ciki. Tana kuma raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasa da kuma dakile yaduwar cutar a lokaci guda, tare da kiyaye rayuka da lafiyar jama’arta yadda ya kamata.

Daga karshen shekarar 2019 zuwa watanni 6 na farkon shekarar 2020, kasar Sin ta gano barkewar annobar a kan lokaci, inda ta tsai da kuduri mai muhimmanci na daukar matakin kulle a birnin Wuhan nan take ba tare da bata lokaci ba, lamarin da ya hana yaduwar cutar zuwa sauran sassan kasar, ta yadda Sin ta tabbatar da daidaiton dakile da kandagarkin cutar a duk fadin kasar, da yin iyakacin kokarin rage asarar rayukan jama’arta. Daga watanni 6 na farkon shekarar 2020 zuwa karshen shekarar 2022, kasar Sin ta yi wa al’ummarta mafi yawa a duniya allurar rigakafin cutar kyauta cikin gajeren lokaci, lamarin da ya sa yawan masu kamuwa da cutar da kuma yawan mutuwar mutane sakamakon cutar dukkansu suka fi kankanta a duniya.

A yayin da kasar Sin take daidaita matsaloli da dama, har kullum tana mara wa kasashen duniya baya wajen yaki da cutar ta COVID-19. Ta samar wa kasashe 153 da kungiyoyin kasa da kasa 15 daruruwan biliyoyin kayayyakin kandagarkin cutar. Ta kuma samar wa kasashe da yankuna fiye da 180 da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 10 fasahohin dakile da kandagarkin cutar da ba da jinya da kiwon lafiya. Kana kuma, kasar Sin ta tura kungiyoyin masana ilmin lafiya 37 zuwa kasashe 34, a kokarin samar da kyawawan fasahohinta na yaki da cutar ba tare da rufa-rufa ba. Har ila yau, kasar Sin ta samar wa kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 120 alluran rigakafin cutar fiye da biliyan 2.2, hakan ya sa kasar Sin zama kasar da ta fi samar wa kasashen duniya alluran.

Tun daga watan Nuwamban shekarar 2022 da ta gabata, kasar Sin ta rika kyautata matakan yaki da cutar, bisa manufar “kiyaye lafiya da magance samun yawan wadanda ke fama da cutar mai tsanani”, ta kuma samu nasara cikin kankanin lokaci, inda aka yi wa mutane fiye da miliyan 200 jinya, tare da ceton wadanda ke fama da cutar mai tsanani kimanin dubu 800. Lamarin da ya sa yawan mutanen da suka mutu sakamakon cutar ya fi kankanta a duk duniya. Kasar Sin ta samu gagarumar nasarar yaki da cutar ta COVID-19, tare da yin abin al’ajabi a tarihin dan Adam. (Tasallah Yuan)

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Majalisar Tarayya Na PDP A Kano Municipal, Da’awah Ya Rabawa Dalibai 500 JAMB

Next Post

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

16 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

17 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

18 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

19 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

20 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

21 hours ago
Next Post
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.