ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

by CMG Hausa
3 years ago
COVID-19

Shekaru 3 bayan barkewar annobar cutar numfashi ta COVID-19 a duniya, kasar Sin tana mayar da jama’arta da rayukansu a gaban kome. Ta kuma kyautata matakan yaki da cutar bisa lokaci da yanayin da ake ciki. Tana kuma raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasa da kuma dakile yaduwar cutar a lokaci guda, tare da kiyaye rayuka da lafiyar jama’arta yadda ya kamata.

Daga karshen shekarar 2019 zuwa watanni 6 na farkon shekarar 2020, kasar Sin ta gano barkewar annobar a kan lokaci, inda ta tsai da kuduri mai muhimmanci na daukar matakin kulle a birnin Wuhan nan take ba tare da bata lokaci ba, lamarin da ya hana yaduwar cutar zuwa sauran sassan kasar, ta yadda Sin ta tabbatar da daidaiton dakile da kandagarkin cutar a duk fadin kasar, da yin iyakacin kokarin rage asarar rayukan jama’arta. Daga watanni 6 na farkon shekarar 2020 zuwa karshen shekarar 2022, kasar Sin ta yi wa al’ummarta mafi yawa a duniya allurar rigakafin cutar kyauta cikin gajeren lokaci, lamarin da ya sa yawan masu kamuwa da cutar da kuma yawan mutuwar mutane sakamakon cutar dukkansu suka fi kankanta a duniya.

A yayin da kasar Sin take daidaita matsaloli da dama, har kullum tana mara wa kasashen duniya baya wajen yaki da cutar ta COVID-19. Ta samar wa kasashe 153 da kungiyoyin kasa da kasa 15 daruruwan biliyoyin kayayyakin kandagarkin cutar. Ta kuma samar wa kasashe da yankuna fiye da 180 da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 10 fasahohin dakile da kandagarkin cutar da ba da jinya da kiwon lafiya. Kana kuma, kasar Sin ta tura kungiyoyin masana ilmin lafiya 37 zuwa kasashe 34, a kokarin samar da kyawawan fasahohinta na yaki da cutar ba tare da rufa-rufa ba. Har ila yau, kasar Sin ta samar wa kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 120 alluran rigakafin cutar fiye da biliyan 2.2, hakan ya sa kasar Sin zama kasar da ta fi samar wa kasashen duniya alluran.

ADVERTISEMENT

Tun daga watan Nuwamban shekarar 2022 da ta gabata, kasar Sin ta rika kyautata matakan yaki da cutar, bisa manufar “kiyaye lafiya da magance samun yawan wadanda ke fama da cutar mai tsanani”, ta kuma samu nasara cikin kankanin lokaci, inda aka yi wa mutane fiye da miliyan 200 jinya, tare da ceton wadanda ke fama da cutar mai tsanani kimanin dubu 800. Lamarin da ya sa yawan mutanen da suka mutu sakamakon cutar ya fi kankanta a duk duniya. Kasar Sin ta samu gagarumar nasarar yaki da cutar ta COVID-19, tare da yin abin al’ajabi a tarihin dan Adam. (Tasallah Yuan)

 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

COVID-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.