• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

by Khalid Idris Doya
3 years ago
kudi

Kwanturolan Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Ƙasa reshen Jihar Bayelsa, CIS Sunday James, ya bayyana cewa tabbas Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, GCFR, ya samu nasarar dakile facaka da kudade da kulakanta dukiya, dakile garkuwa da mutane, wafcen aljihu da sata a manyan hanyoyi, kwacen jakunan mata a kasuwanni da suke rike da kudade a hannunsu.

A cewarsa, yana da kyau al’ummar kasa su fahimci tsare-tsaren kasa da manufofinta tare da bukatun da suka shafi kasa; kasar nan tana tafiya ne bisa doron kundin tsarin mulki da ke jan ragamar kasar, kasar tana da kundin tsarin mulki da sauran dokokin da suke tafiyar da ita.

  • Yadda Daruruwan Dubban Jama’a Suka Halarci Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass Karo Na 37

 

Kana ya ce akwai bukatar bangarorin doka su sake fayyace tsarin sauyin kudi domin kauce wa shafa wa gwamnati bakin fenti, babu wata gwamnatin da za ta dauki wani mataki ba tare da neman shawarorin rassan gwamnati da lamarin ya shafa ba.

kudi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Har ila yau, ya bayyana cewa, don maslahar kasa da hadin kanta, akwai bukatar a daina siyasantar da kowani lamari a kasar nan. An zo lokacin da ba a samun buhuhun kudade ko wadaka da kudade.

Ya kara da cewa, yana da kyau ‘yan Nijeriya su samu masaniyar dalilan sauya kudi. Hakan zai kawo karshen wafcen aljihu, kai hare-hare da balle motoci da gidaje a kowani lokaci domin neman kudi a hannun jama’a.

“A maimakon kushe tsarin, kamatuwa ma ya yi a jinjina ga matakin ba wai yin korafi ko zanga-zanga ba. Yana da kyau mu koyi yadda za mu ke amsar manufofin kasa domin ya fi karfin ra’ayoyin kashin kai.

kudi

“A matsayina na masanin harkokin tsaro, ina shawartar ‘yan Nijeriya da kada su mara baya wa duk wata manufar amfani da kudade ta gurbataccen hanya gabanin babban zaben kasa. Don me gwamnati ba za ta dakile yunkurin sayen kuri’a a lokacin zabe da watsa kudi ba da kuma bai wa jama’a kudi domin sayen ‘yancinsu.

“Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi nasa kuma da bukatar a kara wayar wa al’umma da kai kan muhimmancin wannan sauyin kudin wanda masu kishin kasa za su gane kuma za su mara wa tsarin baya.” Ya bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
Labarai

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
Labarai

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Next Post
Dabarar Siyasa Ta Balan-balan Ta Amurka

Dabarar Siyasa Ta Balan-balan Ta Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.