ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Daruruwan Dubban Jama’a Suka Halarci Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass Karo Na 37

by Umar Faruk
3 years ago
Sheikh Ibrahim Inyass

Dandazon mahalarta

Daruruwan dubban jama’a ne suka yi dafifi a Birnin Kebbi da ke Jihar Kebbi domin halartar Mauludin Sheikh Ibrahim Inyass karo na 37 wanda har ila yau yake nuna cika shekara 137 da haihuwarsa a duniya.

Tun a makon da ya gabata garin Birnin Kebbi ya dauki baki daga Kasashen Afirka ta yamma da kuma mutane daga jihohin Nijeriya da suka yi tattakin zuwa jihar domin halartar taron bikin Mauludin na Sheikh Ibrahim Inyass. Inda hanyoyin mota da gidanjen saukar da baki na babban birnin jihar ya cika makik da mutanen da suka shigo taron Mauludin.

  • Tausayin Annabi Muhammadu (SAW) Ga Al’ummarsa

 

ADVERTISEMENT

Hatta ‘yan kasuwa na waje da na cikin gida Nijeriya ba a bar su a baya ba, domin sun kasa kayyayaki iri daban- daban don sayarwa. Babban taron Mauludin ya gudana ne a filin sukuwa da ke babban birnin jihar.

Da yake jawabi, shugaban kwamitin karbar bakoncin maulidin a Jihar Kebbi, Khalifa Yahaya Bawa Jega ya bayyana jindadinsa ga irin yadda jama’ar Kasashen Afirka da na gida Nijeriya suka yi tattakin zuwa jihar kebbi don gudanar da taron bikin Mauludin na Sheikh Ibrahim Inyass a babban birnin jihar wanda ya ce wannan ba karimain karamci ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Sheikh Ibrahim Inyass
Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass, Shehu Mahi Inyass tare da Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi a wurin maulidin

Ya ce” Muna godiya a madadin ‘yan darikar Tijjaniya na jihar Kebbi. Muna kuma addu’a Allah ya maida kowa gidansa lafiya mun gode.”

Haka zalika ya gode wa gwamnatin jihar da mutanenta kan goyon baya da gudunmuwar da suke bai wa Tijjaniya a jihar.

A nashi ɓangaren, Khalifan Tijjaniyya Nijeriya, Muhammad Sanusi na biyu kuma Sarkin Kano na 14, ya bayyana cewa” makasudin gudanar da toron Mauludin Sheikh Ibrahim Inyass shi ne don tunawa da ranar haihuwar Babban Shehin, da kuma bayyana irin ayyukan da ya gudanar na yada addini da irin fatawa da kuma sauran ayyukan alhairi da ya assasa a cikin duniya. Saboda haka ina kira ga jama’ar mu da muyi koyi da Sheikh Ibrahim Inyass.”

Sheikh Ibrahim Inyass
Khalifa Muhammadu Sanusi II tare da Sayyadi Tijjani Sani Auwalu da aka nada sabon shugaban Kungiyar Majma’u Ahbabu Sheikh Ibrahim Inyass a wurin maulidin

Haka zalika, ya yi kira ga jama’ar musulmi da cewa nan da mako daya mai zuwa za a gudanar da zaben Shugaban kasa da na ‘yan majalisar dattijai saboda irin muhimmanci da ke tattare ga zaben, jama’a ka da su yi kasa a guiwa su tabbatar da sun fito don zaben Shugaban kasa da ‘yan majalisar dattijai da suka dace.

Har ila yau, ya jaddada cewa “akidarmu ita ce yawaita salati da gudanar da zikiri da kuma gode wa Allah. Mu dauki dabi’a hakuri da wanzar da zaman lafiya da kuma yawan bauta wa Allah.

“Nijeriya na bukatar addu’o’i domin kara samun zaman lafiya mai dorewa da samun kwanciyar hankali ga ‘yan kasa. Mu kuma yi addu’a Allah ya sa a yi zabe lafiya a gama lafiya.”

Sheikh Ibrahim Inyass
Dandazon mahalarta

sheikh

Da yake jawabi tun da farko, Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass, Shehu Mahi Ibrahim Inyass ya bayyana jindadinsa da kuma yaba wa mutanen Nijeriya musamman jihar Kebbi inda aka gudanar da taron bikin Mauludin, bisa mutuntawa da ake yi wa Sheikh Ibrahim Inyass da kuma ci gaba da aiwatar da ayyukan da ya yi wa addini.

“Ina godiya a madadin diya da jikoki na gidan Shehu Ibrahim Inyass kan irin soyayar da ake nunawa . Mun gode mun gode.”

sheikh
Shi kuwa Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya yi godiya ga shugabanni kungiyar bisa karamcim da aka yi wa jihar na ba ta damar karbar bakoncin taron Mauludin Sheikh Ibrahim Inyass.

“Jihar Kebbi gidan darikar Tijjaniya ne don haka gwamnatin jihar ba za ta yi mamaki ba don an zabe ta a matsayin wajen da za a gudanar da taron bikin Mauludin Sheikh Ibrahim Inyass na Kasashen Afirka.

A cewarsa, gwamnatin jihar Kebbi za ta ci gaba da ba da goyon baya da gudunmuwarta ga ‘yan darikar don kara samun ci gaban addini da kuma al’ummar mu da kara samun zaman lafiya da tsaro ga jahohin kasar Nijeriya baki daya.

“Bisa ga wannan karancin muna kara godiya ga shugabanni da khalifan Sheikh Ibrahim Inyass da na kasar Nijeriya da sauran duk wadanda suka taimaka aka samu nasarar gudanar da taron bikin.

Daga karshe Gwamnan ya bayyana sakon fatar Alhairi na dan takarar shugaban kasa a Jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Kashim Shatima da Ministan shari’a Abubakar Malami da kuma ba da hakuri ga rashin halartarsu a wajen bikin taron, yana mai cewa” saboda yanayin hazo jirgin su bai iya tasowa ba, wannan shi ne ya hana su halartar bikin. Bisa ga hakan a madadinsu ina mai baku hakuri. Muna godiya kwarai da gaske Allah ya maida kowa gidansa lafiya.”

Haka kuma Gwamna Bagudu ya kara yin game da zaben da ke tafe, yana mai cewar, “Ina kara tunatar da jama’a su fito ranar 25 ga watan 2 na shekara ta 2023 don zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar dattijai sobada muhimmancinsa ga duk ‘yan kasar Nijeriya.

Maulidin na Sheikh Ibrahim Inyass dai ana gudanar da shi ne duk shekara inda ake karbar bakuncinsa a jihohin Nijeriya.

 

sheikh
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
2023: Jam’iyyu 5 Sun Mara Wa Takarar Atiku Baya

2023: Jam’iyyu 5 Sun Mara Wa Takarar Atiku Baya

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.