• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Malamin Darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ayyana goyon bayan takarar Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa a zaben da za a fafata a ranar Asabar.

Sheikh Dahiru ce, zabin Atiku tamkar neman canji ne da halin da al’ummar kasar nan suka samu kansu a karkashin gwamnatin da ke ciki wato APC.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi
  • Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

Atiku dai shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP wanda ke neman kujerar tare da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP, hadi da Peter Obi na LP gami da sauran.

A wani sakon sautin murya na ‘yan dakika da Shehin ya fitar da kuma wakilinmu ya tabbatar da ingancinsa daga hadiman Shehin, Sheikh ya ce, bai dace a cuci mumini har sau biyu a rami daya ba, don haka ne suke naman canji a kasar nan.

A sakon da ya aike wa ‘yan kasa na cewa: “Allah ya kawo mu lokacin zabe, jama’an kasa ‘yan uwana ‘yan Nijeriya. Annabi (S) yana cewa, bai kamata a ciji mumuni sau biyu a rami daya ba. Abu ya cijeka a wannan ramin to ya kamata ka dauki hannunka ka sanya a wani ramin kuma.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

“Sabo da haka na ji wadansu mutane su na cewa a zabi wanda za a zaba ya daura mana a kan inda muka tsaya; to ai inda muka tsayan ba dadi muka ji balle mu daura a kai. Mutum sai ya ji dadi yake cewa a kara a mini, in bai ji dadi ba baya cewa a kara mini.

“Saboda haka ina wa’azi ina kira ina bada shawara a zabi inda za a samu canji ko Allah zai canza mana. Inda muka tsaya ba mu ji dadi ba balle a daura mana a kai.”

Dahiru Bauchi, ya ce, mutanensa sun fitar da Atiku a matsayin dan takararsu, don haka shi ma ya mara musu baya, “Mutane na sun bada shawarar cewa su Atiku za su zaba, ni kuma ba zan rabu da mutane ne ba. Zan nanata mutane ne da suke yin siyasa sun ce Atiku za su zaba tun da ga wanda za su zaba ba zan rabu da su ba ina tare da su. Allah ya zaba mana alkairi.”

Ya yi addu’ar cewa Allah sa a yi zaben lafiya a kammala lafiya kuma Allah sa a zabi shugabanni na kwarai da za su taimaki kasar nan, “Allah sa a samu shugaban da zai ji tausayin talakawa ba kamar yadda muka fito ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuGoyon BayaSheikh Dahiru Usman BauchitakaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masanin NHC:Kusan An Kawo Karshen COVID-19 A Sin

Next Post

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

14 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

20 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin 'Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

LABARAI MASU NASABA

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.