ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Babban Malamin Darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ayyana goyon bayan takarar Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa a zaben da za a fafata a ranar Asabar.

Sheikh Dahiru ce, zabin Atiku tamkar neman canji ne da halin da al’ummar kasar nan suka samu kansu a karkashin gwamnatin da ke ciki wato APC.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi
  • Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

Atiku dai shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP wanda ke neman kujerar tare da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP, hadi da Peter Obi na LP gami da sauran.

ADVERTISEMENT

A wani sakon sautin murya na ‘yan dakika da Shehin ya fitar da kuma wakilinmu ya tabbatar da ingancinsa daga hadiman Shehin, Sheikh ya ce, bai dace a cuci mumini har sau biyu a rami daya ba, don haka ne suke naman canji a kasar nan.

A sakon da ya aike wa ‘yan kasa na cewa: “Allah ya kawo mu lokacin zabe, jama’an kasa ‘yan uwana ‘yan Nijeriya. Annabi (S) yana cewa, bai kamata a ciji mumuni sau biyu a rami daya ba. Abu ya cijeka a wannan ramin to ya kamata ka dauki hannunka ka sanya a wani ramin kuma.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

“Sabo da haka na ji wadansu mutane su na cewa a zabi wanda za a zaba ya daura mana a kan inda muka tsaya; to ai inda muka tsayan ba dadi muka ji balle mu daura a kai. Mutum sai ya ji dadi yake cewa a kara a mini, in bai ji dadi ba baya cewa a kara mini.

“Saboda haka ina wa’azi ina kira ina bada shawara a zabi inda za a samu canji ko Allah zai canza mana. Inda muka tsaya ba mu ji dadi ba balle a daura mana a kai.”

Dahiru Bauchi, ya ce, mutanensa sun fitar da Atiku a matsayin dan takararsu, don haka shi ma ya mara musu baya, “Mutane na sun bada shawarar cewa su Atiku za su zaba, ni kuma ba zan rabu da mutane ne ba. Zan nanata mutane ne da suke yin siyasa sun ce Atiku za su zaba tun da ga wanda za su zaba ba zan rabu da su ba ina tare da su. Allah ya zaba mana alkairi.”

Ya yi addu’ar cewa Allah sa a yi zaben lafiya a kammala lafiya kuma Allah sa a zabi shugabanni na kwarai da za su taimaki kasar nan, “Allah sa a samu shugaban da zai ji tausayin talakawa ba kamar yadda muka fito ba.”

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin 'Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.