• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nishadantar Da Mutane Ya Sa Na Shiga Wasan Barkwanci –Yusuf Abubakar

by Bello Hamza
3 years ago
in Nishadi
0
Nishadantar Da Mutane Ya Sa Na Shiga Wasan Barkwanci –Yusuf Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannna makon mun tattauna ne da wani jarumi mai tasowa a bangaren wasan barkwanci na Kannywood, wato Yusuf Abubakar wanda aka fi sani da Jeje Arewa Commedian. Mataimakin Editanmu Bello Hamza, tattauna da shi ga kuma yadda hirar ta kasance:

Zamu so ka gabatar mana da kanka

Suna na Yusuf Abubakar,mutane kan kira ni Jeje Arewa Comedian

Wanne sana’a kake yi a halin yanzu?

A halin yanzu ina harkar wasan barkwanci ne, wato comedy, da fina finai a takaice dai ni jarumin fina finai ne, zan iya baka dariya a cikin ‘yan sekonni

Labarai Masu Nasaba

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

To menene ya zaburar ko kuma ya karfafa ka har ka shiga wannan harkar?

Da farko dai na ji mutane na cewa, wasan barkwanci abu ne mai kyau, zai iya sa mutane nishadi a kowanne lokaci, na taba ji wani babban jarumi yana cewa, in har mutum ya ji dadin komedy, yana iya sauke wa masu hawan jini ga masu cutar hawan jini, wanann na daga cikin abin da ya kara karfafa ni, na kuma lura da cewa sana’a ce wanda zai iya daukaka ka, in Allah ya dafa maka, to tabbas za ka daukaka

Su wa kake koyi da su a cikin manyan masu wasan barkwanci a masana’antar Kannywood?

Cikin manyan jaruman da ke burgeni a Kannywood su hada da Ali Nuhu da Zango da TK dadin kowa.

Akwai wani kalubale ko tsangwama daga iyaye da abokanan zama da ka fuskanta tunda ka fara wannan harka na barkwanci?

Ba za a rasa kalubale ba amma a wurin iyaye na ban samu mastala ba, don na lura da cewa, a cikin harkar ban yi wani abin da ya saba wa addini ko al’adanmu ba to basu nuna min wani tsangwama ba ko su ce in daina ba.

Ko akwai wani alhairi da ka samu sakamakon wannan harka na wasan barkwanci wanda ba zaka taba mantawa da shi ba?

Lallai akwia alhairai masu yawa da na samu a wasan barkwanci da ba zan taba mantawa da suba, musamman alhairin da Albani ya yi mani, gaskiya mun ji dadi wannan al’amarin sosai, duk da bani kadai ya yi wa ba, a kungiyance ya bamu.

Wanne shawara kake da shi ga matasa musamman wadanda suke sha’awar shiga wannan harkar taku na wasan barkwanci?

Shawarana gare su shi ne su tabbatar da sun jajirce, su kuma sani cewa, sai ka zuba kudin ka  sannan za ka kwashe, sai ka sa kudi da karfi da zuciya da rashin ganin kyashi, da rashin hassada, lallai duk wanda ya je neman shiga wannan sana’ar dole ya nisanci wadannan halayyar.

Akwai wani kira da kake da shi ga gwamnati, nata shigo domin tallafa muku a irin wannan harka da kuke yi na wasan barkwanci, musamman ganin cewa, harkar na sama wa matasa sana’a wanda ke rage zaman kashe wando a tsakanin matasan

Lallai ya kamata gwamnati ta shigo ta taimaka wa matasa masu irin wannan sana’ar, musammna ganin gwamnati za ta amfana da ayyukan matasan, don yawancin gwamnatin ne ke amfana da ayyukan matasa masu irin wannan aikin, inda suka janwo mu a jiki hakan zai kara mana karfin, muna mu ji cewa ana son mu ba wai a cigaba da tsananmu kawai ba.

Wane kira kake da shi ga matasa na su rungumi sana’o’in dogaro da kai komai kankantarsa saboda su tsira da mutuncinsu.

Tabbas zan yi kira ga matasa don ni na ga amfana da sana’a, sana’a na da matukar muhimanci, duk matsalar da ake fuskanta a gari mai sana’a baya rasa abin kashewa a hannunsa, yakamata matasa su rike sana’a komai kankantarsa, sana’a nada muhimmanci ya kuma da dadi.

Menene kololowar burinka a wannan sana’ar, me kake son ka cimma a sana’ar?

Bani da burin da wuce inga Allah ya azurta ni, ko ba ta wanna harkar ba don in taimaki talakawa da iyaye na, burina ke nan a rayuwa gaba daya.

Ina fatan in shahara a duniyar finafnai, kowa ya sanni gaba daya a duniya

Wanne jawabi kake da shi daga karshe?

Ina kira ga manyan a kannywood su rika januyo kananan jarumai masu tasowa a yi tafiyan da su don suma su amfana, a kuma rika gunadar da jarabawa kafin a sanya mutum a fim, hakan zai rage zargin cewa ana nuna son kai wajen sanya matasa a fim, da zargin ko wasu kudi suke bayar wa kafin a sanya su a fim, irin haka ke sa a wadanda basu kwarewa a fim daga baya a rika korafin cewa, fim ya lalace.

Ko akwi zargin cewa, sai an bayar da cin hanci kafin a sanya mutum a fim kenan?

A wasu lokutta a kwai irin wanna zargin, amma zairgi ne kawai da bashi da hajja, don ko muma ana zargin mu da cewa, muna karbar kudi kafin musa matasa a fim, don haka wannan maganar zargi ce kawai

Menene fatan ga Nijeriya?

Ina fatan Allah ya zaunar da kasar mu lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarkwanciKannywoodNishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Next Post

EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja

Related

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

13 hours ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

6 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

4 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Next Post
EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja

EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.