ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nishadantar Da Mutane Ya Sa Na Shiga Wasan Barkwanci –Yusuf Abubakar

by Bello Hamza
3 years ago
Barkwanci

A wannna makon mun tattauna ne da wani jarumi mai tasowa a bangaren wasan barkwanci na Kannywood, wato Yusuf Abubakar wanda aka fi sani da Jeje Arewa Commedian. Mataimakin Editanmu Bello Hamza, tattauna da shi ga kuma yadda hirar ta kasance:

Zamu so ka gabatar mana da kanka

Suna na Yusuf Abubakar,mutane kan kira ni Jeje Arewa Comedian

ADVERTISEMENT

Wanne sana’a kake yi a halin yanzu?

A halin yanzu ina harkar wasan barkwanci ne, wato comedy, da fina finai a takaice dai ni jarumin fina finai ne, zan iya baka dariya a cikin ‘yan sekonni

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

To menene ya zaburar ko kuma ya karfafa ka har ka shiga wannan harkar?

Da farko dai na ji mutane na cewa, wasan barkwanci abu ne mai kyau, zai iya sa mutane nishadi a kowanne lokaci, na taba ji wani babban jarumi yana cewa, in har mutum ya ji dadin komedy, yana iya sauke wa masu hawan jini ga masu cutar hawan jini, wanann na daga cikin abin da ya kara karfafa ni, na kuma lura da cewa sana’a ce wanda zai iya daukaka ka, in Allah ya dafa maka, to tabbas za ka daukaka

Su wa kake koyi da su a cikin manyan masu wasan barkwanci a masana’antar Kannywood?

Cikin manyan jaruman da ke burgeni a Kannywood su hada da Ali Nuhu da Zango da TK dadin kowa.

Akwai wani kalubale ko tsangwama daga iyaye da abokanan zama da ka fuskanta tunda ka fara wannan harka na barkwanci?

Ba za a rasa kalubale ba amma a wurin iyaye na ban samu mastala ba, don na lura da cewa, a cikin harkar ban yi wani abin da ya saba wa addini ko al’adanmu ba to basu nuna min wani tsangwama ba ko su ce in daina ba.

Ko akwai wani alhairi da ka samu sakamakon wannan harka na wasan barkwanci wanda ba zaka taba mantawa da shi ba?

Lallai akwia alhairai masu yawa da na samu a wasan barkwanci da ba zan taba mantawa da suba, musamman alhairin da Albani ya yi mani, gaskiya mun ji dadi wannan al’amarin sosai, duk da bani kadai ya yi wa ba, a kungiyance ya bamu.

Wanne shawara kake da shi ga matasa musamman wadanda suke sha’awar shiga wannan harkar taku na wasan barkwanci?

Shawarana gare su shi ne su tabbatar da sun jajirce, su kuma sani cewa, sai ka zuba kudin ka  sannan za ka kwashe, sai ka sa kudi da karfi da zuciya da rashin ganin kyashi, da rashin hassada, lallai duk wanda ya je neman shiga wannan sana’ar dole ya nisanci wadannan halayyar.

Akwai wani kira da kake da shi ga gwamnati, nata shigo domin tallafa muku a irin wannan harka da kuke yi na wasan barkwanci, musamman ganin cewa, harkar na sama wa matasa sana’a wanda ke rage zaman kashe wando a tsakanin matasan

Lallai ya kamata gwamnati ta shigo ta taimaka wa matasa masu irin wannan sana’ar, musammna ganin gwamnati za ta amfana da ayyukan matasan, don yawancin gwamnatin ne ke amfana da ayyukan matasa masu irin wannan aikin, inda suka janwo mu a jiki hakan zai kara mana karfin, muna mu ji cewa ana son mu ba wai a cigaba da tsananmu kawai ba.

Wane kira kake da shi ga matasa na su rungumi sana’o’in dogaro da kai komai kankantarsa saboda su tsira da mutuncinsu.

Tabbas zan yi kira ga matasa don ni na ga amfana da sana’a, sana’a na da matukar muhimanci, duk matsalar da ake fuskanta a gari mai sana’a baya rasa abin kashewa a hannunsa, yakamata matasa su rike sana’a komai kankantarsa, sana’a nada muhimmanci ya kuma da dadi.

Menene kololowar burinka a wannan sana’ar, me kake son ka cimma a sana’ar?

Bani da burin da wuce inga Allah ya azurta ni, ko ba ta wanna harkar ba don in taimaki talakawa da iyaye na, burina ke nan a rayuwa gaba daya.

Ina fatan in shahara a duniyar finafnai, kowa ya sanni gaba daya a duniya

Wanne jawabi kake da shi daga karshe?

Ina kira ga manyan a kannywood su rika januyo kananan jarumai masu tasowa a yi tafiyan da su don suma su amfana, a kuma rika gunadar da jarabawa kafin a sanya mutum a fim, hakan zai rage zargin cewa ana nuna son kai wajen sanya matasa a fim, da zargin ko wasu kudi suke bayar wa kafin a sanya su a fim, irin haka ke sa a wadanda basu kwarewa a fim daga baya a rika korafin cewa, fim ya lalace.

Ko akwi zargin cewa, sai an bayar da cin hanci kafin a sanya mutum a fim kenan?

A wasu lokutta a kwai irin wanna zargin, amma zairgi ne kawai da bashi da hajja, don ko muma ana zargin mu da cewa, muna karbar kudi kafin musa matasa a fim, don haka wannan maganar zargi ce kawai

Menene fatan ga Nijeriya?

Ina fatan Allah ya zaunar da kasar mu lafiya.

Barkwanci
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja

EFCC Ta Kama Wasu Masu Sayen Katin Zabe A Kano, Kaduna Da Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.