• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kaddamar da rabon Naira miliyan dari biyar (N500,000,000) a matsayin tallafi ga kungiyoyin ‘yan kasuwa daban-daban a Jihar Gombe don taimaka musu wajen sake inganta sana’o’i da kasuwancin su da kuma shawo kan matsalar tabarbarewar tattalin arziki da annobar Korona ta haifar. 

 

Wannan karimcin na zuwa ne a karkashin shirin farfado da tattalin arzikin Jihar Gombe na COVID-19 da ake kira GO-CARES, wanda shirin tallafi ne na gwamnatin jihar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe DPO Da Wani Dan Sanda A Zamfara

Da ya ke jawabi a wajen bikin kaddamar da shirin, gwamnan yakce, gwamnatin sa ta himmatu matuka wajen magance kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar jihar wanda shi ne dalilin kafa gidauniyar farfado da tattalin arzikin Nijeriya wato NG-CARES na Gwamnatin Tarayya a Jihar Gombe inda aka ware sama da Naira biliyan 8 da miliyan 500 don tallafawa magidanta 288,700 da manoma da masu kananan sana’o’i a lungu da sako na jihar domin dakile barnar da cutar Korona ta yi ga tattalin arzikin kasa da rayuwar al’ummar duniya.

Inuwa

Labarai Masu Nasaba

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Ya ce, tun bayan kaddamar da shirin a watan Yulin shekarar da ta gabata, shirin na GO-CARES ya kashe kimanin Naira biliyan 3 da miliyan 400 ta hanyar ayyuka daban-daban da kuma tallafin daya kai ga dubban iyalai da ‘yan kasuwa masu rauni.

 

“Ya zuwa yanzu, ‘yan asalin Jihar Gombe dubu 147 da 666 ne suka ci gajiyar wannan shirin na GO-CARES kuma za a sanya karin wassu da dama nan gaba. Namu tallafi ne ba rance ba, kuma rabon wannan makudan kudade shaida ce ta yadda muke daukar sana’o’i da muhimmanci saboda irin rawar da suke takawa wajen ci gaban jihar mu”.

 

Gwamnan ya bayyana cewa ajandar ci gaban da gwamnatin sa ke aiwatarwa ta hanyar zurfafa zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa da samar da ci gaban jama’a ya samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa, inda ya bada misali da hanyoyi a rukunin masana’antu na Nasarawo da babbar kasuwar Gombe da fitulun hanya masu amfani da hasken rana da inganta tsaro da sauran su.

 

Tun da farko a jawabin sa na maraba, kwamishinan ciniki, masana’antu da yawon shakatawa, Hon. Nasiru Aliyu ya ce, gwamnatin Inuwa zata ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa don dawo da martabar kasuwanci.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan Matasa Hon. Abubakar Aminu Musa, ya ce shirin na GO-CARES ya ceto iyalai da ‘yan kasuwa da dama a fadin jihar ta hanyar tsare-tsaren sa daban-daban, inda ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su bada goyon bayan ci gaba da shirin ta hanyar sake zabar Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.

 

Da suke jawabi a madadin ‘yan kasuwan da suka amfana, Alhaji Sunusi Abdullahi Mai Agogo da Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kafa waje Alhaji Uba Abdullahi da Shugabar Mata ‘yan Kasuwa Dr. Eliza Danladi da Shugaban hadin kan kungiyar ‘yan kasuwa ta Amalgamated, Alh. Abba Bill Gates, sukace Gwamna Inuwa ya cika alkawuran daya dauka na tallafawa ‘yan kasuwa, suna masu godiya bisa wannan karimcin, tare da bada tabbacin yin amfani da tallafin yadda ya kamata.

Inuwa

Sun kuma yi alkawarin ci gaba da bai wa gwamnan goyon baya, tare da yi masa alkawarin zasu ramawa kura aniyar ta a zabe mai zuwa domin dorewar ayyukan raya ƙasa da kuma maslahar Jihar Gombe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Next Post

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

Related

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

49 minutes ago
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025
Labarai

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

2 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

5 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

6 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Manyan Labarai

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

7 hours ago
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3
Manyan Labarai

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

10 hours ago
Next Post
Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.