ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kaddamar da rabon Naira miliyan dari biyar (N500,000,000) a matsayin tallafi ga kungiyoyin ‘yan kasuwa daban-daban a Jihar Gombe don taimaka musu wajen sake inganta sana’o’i da kasuwancin su da kuma shawo kan matsalar tabarbarewar tattalin arziki da annobar Korona ta haifar. 

 

Wannan karimcin na zuwa ne a karkashin shirin farfado da tattalin arzikin Jihar Gombe na COVID-19 da ake kira GO-CARES, wanda shirin tallafi ne na gwamnatin jihar.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe DPO Da Wani Dan Sanda A Zamfara

Da ya ke jawabi a wajen bikin kaddamar da shirin, gwamnan yakce, gwamnatin sa ta himmatu matuka wajen magance kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar jihar wanda shi ne dalilin kafa gidauniyar farfado da tattalin arzikin Nijeriya wato NG-CARES na Gwamnatin Tarayya a Jihar Gombe inda aka ware sama da Naira biliyan 8 da miliyan 500 don tallafawa magidanta 288,700 da manoma da masu kananan sana’o’i a lungu da sako na jihar domin dakile barnar da cutar Korona ta yi ga tattalin arzikin kasa da rayuwar al’ummar duniya.

Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce, tun bayan kaddamar da shirin a watan Yulin shekarar da ta gabata, shirin na GO-CARES ya kashe kimanin Naira biliyan 3 da miliyan 400 ta hanyar ayyuka daban-daban da kuma tallafin daya kai ga dubban iyalai da ‘yan kasuwa masu rauni.

 

“Ya zuwa yanzu, ‘yan asalin Jihar Gombe dubu 147 da 666 ne suka ci gajiyar wannan shirin na GO-CARES kuma za a sanya karin wassu da dama nan gaba. Namu tallafi ne ba rance ba, kuma rabon wannan makudan kudade shaida ce ta yadda muke daukar sana’o’i da muhimmanci saboda irin rawar da suke takawa wajen ci gaban jihar mu”.

 

Gwamnan ya bayyana cewa ajandar ci gaban da gwamnatin sa ke aiwatarwa ta hanyar zurfafa zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa da samar da ci gaban jama’a ya samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa, inda ya bada misali da hanyoyi a rukunin masana’antu na Nasarawo da babbar kasuwar Gombe da fitulun hanya masu amfani da hasken rana da inganta tsaro da sauran su.

 

Tun da farko a jawabin sa na maraba, kwamishinan ciniki, masana’antu da yawon shakatawa, Hon. Nasiru Aliyu ya ce, gwamnatin Inuwa zata ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa don dawo da martabar kasuwanci.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan Matasa Hon. Abubakar Aminu Musa, ya ce shirin na GO-CARES ya ceto iyalai da ‘yan kasuwa da dama a fadin jihar ta hanyar tsare-tsaren sa daban-daban, inda ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su bada goyon bayan ci gaba da shirin ta hanyar sake zabar Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.

 

Da suke jawabi a madadin ‘yan kasuwan da suka amfana, Alhaji Sunusi Abdullahi Mai Agogo da Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kafa waje Alhaji Uba Abdullahi da Shugabar Mata ‘yan Kasuwa Dr. Eliza Danladi da Shugaban hadin kan kungiyar ‘yan kasuwa ta Amalgamated, Alh. Abba Bill Gates, sukace Gwamna Inuwa ya cika alkawuran daya dauka na tallafawa ‘yan kasuwa, suna masu godiya bisa wannan karimcin, tare da bada tabbacin yin amfani da tallafin yadda ya kamata.

Inuwa

Sun kuma yi alkawarin ci gaba da bai wa gwamnan goyon baya, tare da yi masa alkawarin zasu ramawa kura aniyar ta a zabe mai zuwa domin dorewar ayyukan raya ƙasa da kuma maslahar Jihar Gombe.

Inuwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.