ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kisan Kai: Kotu Ta Bayar Da Belin Alhassan Ado Doguwa Kan Miliyan N500

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Doguwa

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a, Muhammad Nasir Yunusa, ta bayar da belin shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai ta kasa, Alhassan Garba Ado Doguwa kan kudi naira miliyan 500.

Kaalika, Kotun ta umarci Doguwa da ya gabatar da wasu masu tsaya masa mutum biyu da darajarsu ya kai wannan kudin.

  • An Kama Alhassan Doguwa Kan Zargin Kisan Kai A Kano
  • Jama’ar Tudun Wada Na Zanga-Zanga Kan A Yi Adalci A Zargin Kisa Da Ake Wa Doguwa

Doguwa na fuskantar shari’a ne kan zarge-zargen aikata manyan laifuka da suka kunshi hada baki, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, kisan kai da kuma tada husuma a cikin al’uma.

ADVERTISEMENT

Sai dai Alhassan bai amince kan cewa ya aikata laifukan ba lokacin da aka gurfanar da shi a gaban kotun majistire mai lamba 54 da ke Kano a makon jiya.

Lauyansa da ke ba shi kariya, Nuraini Jimoh (SAN), a ranar Litinin ya roki babban kotun tarayya da ke zamanta a Kano da ta amince da bayar da belin Doguwa, yana mai cewa ana kyautata zaton cewa wanda ake zargin bai da wani laifi lura da sashi na 35 na karamin sashi na 6 na kudin tsarin mulkin kasa (1999 da aka yi wa garanbawul).

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Da ya ke yanke hukunci kan rokin, Alkalin Nasir Yunusa, ya amince da bayar da belin kan naira miliyan 500 da wasu mutum biyu masu daraja kamar ta kudin.

A cewar kotun, masu tsaya masa dole ne su kasance sarki mai daraja ta 1 ko manyan jami’an gwamnati.

Kotun ta kuma umarci Alhassan Doguwa da ya ajiye fasfo dinsa na fita kasar waje a wajen rijistaran kotun har zuwa kammala shari’ar.

Kotun ta kuma haramta wa Alhassan Doguwa zuwa mazabarsa a lokacin zaben gwamna da na ‘yan majalisun jihohi da ke tafe a ranar11 ga watan Maris na 2023.

LEADERSHIP ta rawaito cewa, kotun majistire karkashin Ibrahim Mansur Yola, a ranar Larabar da ta gabata ya tura Alhassan Doguwa zuwa gidan yarin Goron Dutse bisa zarge-zargen da ake masa bayan kama shi da ‘yansanda suka yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Sin Za Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Zamantakewa Da Tattalin Arziki

Sin Za Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Zamantakewa Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.