• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta bukaci hukumomin tsaro da su samar da zaman lafiya ba tare da tashin hankali ba a ranar 11 ga Maris a jihar.

Wani jigo a jam’iyyar Dokta Bappa Bichi ne ya yi wannan roko a ranar Litinin a wani taron manema labarai a Kano.

  • Wike Ya Yi Wa Atiku Shagube Kan Zanga-Zangar Neman INEC Ta Soke Zaben Shugaban Kasa
  • Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya

Bichi ya ce sha’awar ‘yan Nijeriya na zaben shugabannin da suke so ba zai yiwu ba idan hukumomin tsaro suka gaza samar da daidaito ga dukkanin jam’iyyun siyasa.

A cewarsa, hakan zai ba da damar gudanar da zabe na gaskiya da adalci.

Ya kuma bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da hukumomin tsaro da su kasance ‘yan ba ruwana kuma masu gaskiya da kuma rashin nuna bangaranci wajen gudanar da ayyukansu a lokacin da kuma bayan kammala aikin.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

A cewarsa, jam’iyyar NNPP jam’iyya ce mai son zaman lafiya kuma tana gudanar da ayyukanta ba tare da wani tashin hankali na siyasa da ‘yan daba ba.

“Bari na yi amfani da wannan dama wajen tabbatar da cewa jam’iyyarmu ta NNPP ba za ta iya ba kuma ba za ta taba mika wuya ga tsoratarwa ko barazana ga kowa ba.

“Ba za mu zauna a banza muna kallon yadda ake cin zarafi da cin mutuncin mambobinmu ba, da tsoratarwa daga gwamnati ba tare da wani dalili ba,” in ji jigon jam’iyyar.

A cewarsa, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa an samar da fili daidai gwargwado ga duk masu ruwa da tsaki da suka cancanta domin shiga zaben ba tare da barazana ga rayuka da dukiyoyi ba.

“Ba za mu taba bari a sace muradin mutane ba. Sun kwace mana iko a 2019. Mun hana magoya bayanmu tare da hana su fitowa kan tituna suna zanga-zangar.

Ya yi gargadin “A wannan karon zai yi wahala mu bari sake takurawa magoya bayanmu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCJami'an TsarokanoMagudiNNPPZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 

Next Post

An Fara Bincike Kan Sojan Da Ya Kashe Abokin Aikinsa, Ya Kuma Hallaka Kansa A Sakkwato 

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

50 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

2 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

3 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

5 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

11 hours ago
Next Post
An Fara Bincike Kan Sojan Da Ya Kashe Abokin Aikinsa, Ya Kuma Hallaka Kansa A Sakkwato 

An Fara Bincike Kan Sojan Da Ya Kashe Abokin Aikinsa, Ya Kuma Hallaka Kansa A Sakkwato 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.