• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan takaran gwamnan Jihar Gombe su takwas daga jam’iyyun adawa daban-daban sun mara tazarcen gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya baya, tare da yin alkawarin taya shi aiki don samun nasara a zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da ke tafe ranar Asabar.

Shugaban gamayyar tuntuba tsakanin jam’iyyun siyasa na jihar (IPAC) kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar Zenith Labour Party, Muhammad Gana Aliyu shi ne ya bayyana hakan yayin wata zantawa da manema labarai a ofishin sa dake Gombe.

  • Dan Bindiga Ya Shiga Hannu, Ya Bayyana Yadda Ya Kashe Mutum 15 A Katsina
  • Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

Ya ce, sun dauki matakin ne bayan doguwar tattaunawa da nazari kan nasarorin da gwamnati mai ci ta samu a karkashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

Ya ce, “Mun cimma wannar muhimmiyar matsaya ce bayan da muka yi nazari sosai kan yadda Gwamna Inuwa yake gudanar da ayyukan sa musamman ta fuskar samar da zaman lafiya, da tsaro da ilimi, da kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa da ayyukan jinlai a faɗin jihar”.

Shugaban na IPAC ya ce, ‘yan takaran da suka mara baya ga gwamnan na Gombe kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar APC su ne: Muhammad Gana Aliyu na Jam’iyyar Zenith Labour Party (ZLP), da Sulaiman Abubakar Sunusi na Jam’iyyar National Rescue Movement (NRM), da Sadiq Abdulhamid na Jam’iyyar Boot Party (BP) da Adamu Muhammad na Jam’iyyar Action Peoples Party (APP).

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Sauran sun hada da Sulaiman Jibrin na Jam’iyyar Action Democratic Party (ADP), da Adamu Aliyu Ɗanmakka na Jam’iyyar African Action Congress (AAC), sai Kelmi Jacob Lazarus na Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da Muhammad Bello Abubakar na Jam’iyyar Allied Peoples Party (APP).

‘Yan takaran sun kuma yi kira ga magoya bayan su dasu zabi Gwamna Inuwa Yahaya don ba shi damar dorawa kan yunkurin sa na samar da ayyukan ci gaba mai ɗorewa a jihar.

‘Yan takaran gwamnan takwas da suka amincewa Gwamna Inuwa suna daga cikin ‘yan takara 13 da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya wadda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) da hadin gwiwar Kwamitin Tuntuba Tsakanin Hukumomi Kan Harkokin Tsaro (ICCES) suka shirya a ranar 15 ga watan Fabrairun wannar shekara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Bindiga Ya Shiga Hannu, Ya Bayyana Yadda Ya Kashe Mutum 15 A Katsina

Next Post

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
Gombe
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam'iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Gombe

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.