ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

‘Yan takaran gwamnan Jihar Gombe su takwas daga jam’iyyun adawa daban-daban sun mara tazarcen gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya baya, tare da yin alkawarin taya shi aiki don samun nasara a zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da ke tafe ranar Asabar.

Shugaban gamayyar tuntuba tsakanin jam’iyyun siyasa na jihar (IPAC) kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar Zenith Labour Party, Muhammad Gana Aliyu shi ne ya bayyana hakan yayin wata zantawa da manema labarai a ofishin sa dake Gombe.

  • Dan Bindiga Ya Shiga Hannu, Ya Bayyana Yadda Ya Kashe Mutum 15 A Katsina
  • Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

Ya ce, sun dauki matakin ne bayan doguwar tattaunawa da nazari kan nasarorin da gwamnati mai ci ta samu a karkashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Mun cimma wannar muhimmiyar matsaya ce bayan da muka yi nazari sosai kan yadda Gwamna Inuwa yake gudanar da ayyukan sa musamman ta fuskar samar da zaman lafiya, da tsaro da ilimi, da kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa da ayyukan jinlai a faɗin jihar”.

Shugaban na IPAC ya ce, ‘yan takaran da suka mara baya ga gwamnan na Gombe kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar APC su ne: Muhammad Gana Aliyu na Jam’iyyar Zenith Labour Party (ZLP), da Sulaiman Abubakar Sunusi na Jam’iyyar National Rescue Movement (NRM), da Sadiq Abdulhamid na Jam’iyyar Boot Party (BP) da Adamu Muhammad na Jam’iyyar Action Peoples Party (APP).

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Sauran sun hada da Sulaiman Jibrin na Jam’iyyar Action Democratic Party (ADP), da Adamu Aliyu Ɗanmakka na Jam’iyyar African Action Congress (AAC), sai Kelmi Jacob Lazarus na Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da Muhammad Bello Abubakar na Jam’iyyar Allied Peoples Party (APP).

‘Yan takaran sun kuma yi kira ga magoya bayan su dasu zabi Gwamna Inuwa Yahaya don ba shi damar dorawa kan yunkurin sa na samar da ayyukan ci gaba mai ɗorewa a jihar.

‘Yan takaran gwamnan takwas da suka amincewa Gwamna Inuwa suna daga cikin ‘yan takara 13 da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya wadda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) da hadin gwiwar Kwamitin Tuntuba Tsakanin Hukumomi Kan Harkokin Tsaro (ICCES) suka shirya a ranar 15 ga watan Fabrairun wannar shekara.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam'iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.