ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

by Sadiq
3 years ago
Kotu

Wata babbar kotun jiha da ke zamanta a Owerri, babban birnin jihar Imo, ta yanke wa tsohon kwamishinan sufuri a karkashin gwamnatin Rochas Okorocha, Laz Okoroafor-Anyanwu, hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, bayan da aka same shi da laifukan da suka shafi zamba da sata.

Da ta ke yanke hukuncin, alkalin kotun, Mai shari’a K.A Lewanya, ya ce Okoroafor-Anyanwu an same shi da laifin karkatar da Naira miliyan 180 na kudaden jihar zuwa asusun wani kamfani mai zaman kansa.

  • Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar
  • Birnin Beijing Zai Kara Yawan Lambunan Shakatawa

Alkalin ta ce ya kasance babban mai hannun jari a kamfanin.

ADVERTISEMENT

A cewar mai shari’a, Okoroafor-Anyanwu an kuma same shi da laifin karya dokar siyan kaya, cin zarafin ofis, da kuma yin amfani da ofishinsa wajen samun tagomashi da bai dace ba a cikin harkokinsa a lokacin da yake rike da mukamin kwamishina.

Ya ce lauyan Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Barista Michael Ani, wanda shi ne lauyan mai shigar da kara ya tabbatar da babu shakka cewa lokacin da Okoroafor-Anyanwu yake kwamishinan a tsakanin 2015 zuwa 2019, ya mika zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 daga asusun ITC zuwa kamfanin mai zaman kansa mai suna Oma Oil Industries Limited wanda ya sabawa sashe na 12 da 19 na dokar ICPC ta 2020 na ma’aikacin gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Alkalin kotun ta kara da cewa, a irin wannan hali, Okoroafor-Anyanwu ya sanya hannu a kan wasu kudi har Naira miliyan 80 daga asusun gwamnati kai tsaye zuwa asusun kamfaninsa mai zaman kansa kan cewa zai sayo wasu motoci don gudanar da ayyuka ba tare da bin ka’ida da bin doka da oda na ma’aikatan gwamnati ba.

Ko da yake Okoroafor-Anyanwu ya ki amsa laifinsa, alkalin da ta yanke hukuncin daurin shekara daya a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Alkalin ta kuma yanke hukuncin cewa kudin da aka wawure Naira miliyan 180 da aka samu a asusunsa, a mika su ga Kamfanin Sufuri na Jihar Imo.

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.