• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum 17 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu karin mutane 17 suka jikkata a tagwayen hatsarin mota da suka faru a wurare daban-daban a Bauchi a ranar Litinin.

Mutum sha daya ne suka mutu a hatsari farko, yayin da wasu shida kuma suka rasa rayukansu a hatsarin na biyu.

  • Dan Bindiga Ya Shiga Hannu, Ya Bayyana Yadda Ya Kashe Mutum 15 A Katsina
  • ‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya

Kamar yadda rahoton RS12.11 na ofis din ke kula da Azare zuwa Gamawa na hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) reshen jihar Bauchi, hatsarin farko ya faru ne a kauyen Manaba da ke hanyar Zaki zuwa Gamawa da ya shafi mutum 25.

Hatsarin ya ci rayukan mutum 11, manyan Maza 2 da manyan mata 9, sannan wasu 13 kuma suka jikkata Maza manya 3 da mata manya 10.

Hatsarin da ya faru sakamakon fashewar tayar mota kirar Toyota Hummer Mai lamba KTG 13XF ta kabu-kabu da wani direba mai suna Haruna Yusuf ke tukawa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

A cewar rahoton FRSC, hatsarin ya faru ne sakamakon lodin ganganci, gudun wuce kima, fashewar tayar motar da har hakan ya sanya direban ya kasa iya shawo kan motar duk da cewa hanyar titin simul garau yake.

Daga bisani an kwashi wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Gamawa.

Kazalika, hatsarin na biyu da ya ci rayukan mutum shida yayin da wasu hudu suka gamu da munanan raunuka.

A cewar rahoton RS12. 12 na ofishin hukumar kiyaye aukuwar hadura FRSC a Shira da ke jihar Bauchi dauke da sanya hannun DRC, TB Lawal, STO Shira, na cewa hatsarin ya faru ne a hanyar Yana zuwa Giade da ke da tazarar kilomita 10 da cikin kwaryar Yana a karamar hukumar Shira.

Hatsarin da ya hada da motoci biyu na kabu-kabu kirar Volkswagen Golf 2 da suka yi taho mu gama da wata karamar bus din Sharon mai dauke da lamba SHR 203 AA yayin da dayan motar Kuma ba ta da lamba a jikanta da wani mutum Alhaji Bappah Adamu Nasarawa ke tukawa.

A cewar FRSC, Kila hatsarin ya faru ne sakamakon gudun ganganci da ya janyo mutuwar mutum 6, manyan Maza 4 da manyan mata 2 yayin da wasu 10 suka gamu da raunuka daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiFRSCHatsarin Mota
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

Next Post

Gobarar Kano: ‘Yan Kasuwar Singa Na Neman Tallafi Daga Gwamnatin Tarayya

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 hours ago
Hatsarin Mota
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Gobarar Kano: ‘Yan Kasuwar Singa Na Neman Tallafi Daga Gwamnatin Tarayya

Gobarar Kano: 'Yan Kasuwar Singa Na Neman Tallafi Daga Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.