• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani sabon harin da aka kai unguwar Langson da ke karamar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna, an tabbatar da mutuwar mutane akalla 10 tare da jikkata wasu da dama.

Harin wanda aka ce ya faru ne a daren ranar Talata har zuwa wayewar safiyar Laraba, an ce ya faru ne duk da dokar hana fita ta sa’o’i 24 da aka kafa bayan harin da aka kai a makon jiya da ya yi sanadin mutuwar mutane 17.

  • ‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfara 21 A Abuja

A halin da ake ciki kuma, shugabannin kungiyar ci gaban al’ummar Atyap (ACDA), wadanda suka tabbatar da harin na baya-bayan nan, sun nuna rashin amincewa da jami’an tsaron da aka tura yankin domin kare rayuka da dukiyoyinsu.

Shugaban ACDA na kasa, Mista Sam Achie, ya ce, “’Yansandan tsaro da aka tura Kudancin Kaduna ba su ba mu kariya, domin an dade ana kashe-kashe ba tare da la’akari da hakan ba, amma gwamnati ta yi shiru.

Achie, wanda ya bayyana hakan a wurin da aka kai harin a lokacin da ya kai ziyara, ya jaddada cewa shiru da gwamnatin jihar Kaduna ta yi kan ci gaba da kai hare-hare a yankin abin damuwa ne.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Don haka ya bukaci gwamnati dauki matakin kawo karshen hare-haren.

Shugaban ACDA na kasa, ya yabawa rundunar MOPOL da ke yankin Langson, wanda aka ce sun fatattaki maharan, yayin da ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da kasancewa cikin shiri domin kare kan su da dukiyoyinsu daga azzalumai.

Ya bayyana cewa wadanda suka jikkata a harin na samun kulawa a wasu asibitocin yankin.

A nasa bangaren, shugaban karamar hukumar Zango Kataf, Mista Francis Sani, wanda shi ma ya tabbatar da faruwar harin, ya roki gwamnatin jihar da ta kara tura jami’an tsaro zuwa karamar hukumar Zango Kataf, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.

LEADERSHIP ta tattaro, cewar maharan sun mamaye al’ummar garin ne da misalin karfe 9 na daren ranar Talata, inda suka yi ta harbe-harbe inda suka kashe jama’a, tare da raunata wasu, tare da yin awon gaba da wani mai shago a yankin, kafin daga bisani MOPOL suka fatattake su.

Kakakin rundunar Operation Safe Haven, Laftanar Kanar I.S. Takwa, bai amsa waya ba don jin ta bakinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKisaMaharaYan bindigaZangon Kataf
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Next Post

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Related

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

1 day ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

2 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

2 days ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

2 days ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

3 days ago
Next Post
Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.