• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 1 ga watan Maris 2023 ne Hukumar Zabe INEC ta bayyana jam’iyya mai mulki ta APC a matsayin wadanda ta lashe zaben shugaban kasa da aka yi ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu 2023.

Tinubu, tsohon gwamnan Jihar Legas wanda ya yi wa APC takara ya samu kuri’u 8,794,726 inda ya kayar da Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 6,984,520.

  • Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi
  • An Fitar Da Tsarin Yin Kwaskwarima Na JKS Da Hukumomin Gwamnati

Wanda ya zo na uku a zaben shi ne Peter Obi na jam’iyyar LP mai kuri’a 6,101,533 sai kuma Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP wanda ya zo na hudu da kuri’u 1,496,687.

A ranar da aka yi zaben shugaban kasa, ‘yan Nijeriya sun kuma zabi ‘yan majalisun kasa 469, da yawa a cikin su kuma wannan ne karo na farko na shigarsu majalisar.

Amma kuma zaben shugaban kasa, kamar dai yadda aka yi a shekarun baya, a wannan karon ma yana tattare ne da abubuwan da sukia shafi kabilanci da addini, musamman ma ganin dukkan manyan ‘yan takarar su uku sun fito ne daga manyan kabilun kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Sannan kuma wadanda suka zo na biyu da na uku duk suna ikirarin sune suka lashe zaben, suna korafin cewa an yi magudi a yayin da ake tattara sakamakon zaben. Baya ga hukuncin kotun da ke sauraren karrarikin zabe da kuma hukuncin da kotun koli za ta iya yankewa daga baya babu wata dokar da za ta iya hana a rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

Da zarar ya dare karagar mulki, zai shiga hidimar zabo ministoci da shugabanin ma’aikatu da za su taimaka masa wajen aiwatar da alkawurran da ya yi wa al’ummar Nijeriya a lokacin da yake yakin neman zabe, shugaban kasan zai kuma iyan tabbatar da ganin wanene zai zama shugaban majalisar dadttawa da kuma ta wakilai. A kan haka ne muke ganin yana da matukar muhimmanci a ra’ayinmu na mu jawo hankalin shugaban kasa Tinubu a kan bukatar a samar da gwamnatin da dukkan bangarorin kasa za su san ana damawa su a cikin gwamnatin da kuma shugabanin majalisar kasa. A siyasance, Tinubu ya kafa harkar siyasan ce a yankin kudu maso yammacin Nijeriya. Kuma kamar yadda ne bayyana da bakinsa, ya kuduri burin zama shugaban kasa ne a dukkan tsawon rayuwarsa. Tabbas wannan burinasa ne ya sanya ya yi watsi da jam’iyyar ACN inda ya shiga hadaka da jam’iyyar APC, jam’iyyar da ke da asali daga yankin arewacin Nijeriya.

A wannan hadakar a gwamnatin da ta gabata, a ware wasu yankuna a yayin zaben shugabanin majalisar kasa, yayin da arewa ta samu shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, yankin kudu maso yamma suka samu mataimaki shugaban kasa da shugaban majalisar wakilai, muna kira ga zabbaben shugaban kasa da kada ya bi wannan hanyar.

Amma daga dukkan alamu, bangaren shugaban kasa basu kammala bukuwan lashe zabe ba, amma sai gashi har an fara gwagwamaryar neman shugabancin majalisan dattawa da kuma ta Wakilai.

Duk da cewa, a boye ake kamun kafar neman shugabancin majalisun biyu, amma al’umma na ganin yadda al’amurran ke tafiya, inda ake yi wa wasu ‘yan majalisar kamun kafa da yawa na amfanin da makaman da ke a hannun su wadanda suka hada da bukatar da yankunan suke cii na neman ayyukan cigaba, zamu ga wasu irin wadannan salon kamun kafar daga masu neman shugabancin majalisar kasa a nan gaba kada.

Akwai wasu tanade-tanade a cikin kundin tsarin mulkin kasa da aka tabbatar da cewa, ba a juya wa wani bangare ko jiha baya ba a harkar gudanar da kasa.  Baya ga tabbatar da shugaban kasa ya zabi Ministoci daga dukkan jihohin tarayyar kasar nan, tsarin mulki ya fayyace yadda za a kafa gwmanatin tarayya da ma na wasu ma’aikatun  gwamnati ta yadda za a tafi tare da kowa da kowa don samar da hadin kan kasa.

Da babu wannan tanadin da Tinubu yana da damar ya zabi ‘yan asalin jiharsa ta Legas su zama ministoci maimakon ya zaba daga jihohi 36 a tarayyar Nijeriya, sai dai a wuraren da ba a samu wadanda suka cancaci rike wani mukami ba daga wata jiha. Doka ta tanadi a rarraba mukamai a tsakanin shiyoyyin siyasa shida na kasar nan don kowa ya san ana damawa da shi. Don haka a kwai bukatar a yi takatsantsan wajen ganin kowacce bangare na kasa ya samu wakilci a dukkan bangarorin gudanar da mukin kasar nan gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Hadin KaiINECLegasTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Next Post

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Related

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

3 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

8 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

22 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

1 day ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.