ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

by Leadership Hausa
3 years ago
Hadin Kai

A ranar 1 ga watan Maris 2023 ne Hukumar Zabe INEC ta bayyana jam’iyya mai mulki ta APC a matsayin wadanda ta lashe zaben shugaban kasa da aka yi ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu 2023.

Tinubu, tsohon gwamnan Jihar Legas wanda ya yi wa APC takara ya samu kuri’u 8,794,726 inda ya kayar da Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 6,984,520.

  • Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi
  • An Fitar Da Tsarin Yin Kwaskwarima Na JKS Da Hukumomin Gwamnati

Wanda ya zo na uku a zaben shi ne Peter Obi na jam’iyyar LP mai kuri’a 6,101,533 sai kuma Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP wanda ya zo na hudu da kuri’u 1,496,687.

ADVERTISEMENT

A ranar da aka yi zaben shugaban kasa, ‘yan Nijeriya sun kuma zabi ‘yan majalisun kasa 469, da yawa a cikin su kuma wannan ne karo na farko na shigarsu majalisar.

Amma kuma zaben shugaban kasa, kamar dai yadda aka yi a shekarun baya, a wannan karon ma yana tattare ne da abubuwan da sukia shafi kabilanci da addini, musamman ma ganin dukkan manyan ‘yan takarar su uku sun fito ne daga manyan kabilun kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sannan kuma wadanda suka zo na biyu da na uku duk suna ikirarin sune suka lashe zaben, suna korafin cewa an yi magudi a yayin da ake tattara sakamakon zaben. Baya ga hukuncin kotun da ke sauraren karrarikin zabe da kuma hukuncin da kotun koli za ta iya yankewa daga baya babu wata dokar da za ta iya hana a rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

Da zarar ya dare karagar mulki, zai shiga hidimar zabo ministoci da shugabanin ma’aikatu da za su taimaka masa wajen aiwatar da alkawurran da ya yi wa al’ummar Nijeriya a lokacin da yake yakin neman zabe, shugaban kasan zai kuma iyan tabbatar da ganin wanene zai zama shugaban majalisar dadttawa da kuma ta wakilai. A kan haka ne muke ganin yana da matukar muhimmanci a ra’ayinmu na mu jawo hankalin shugaban kasa Tinubu a kan bukatar a samar da gwamnatin da dukkan bangarorin kasa za su san ana damawa su a cikin gwamnatin da kuma shugabanin majalisar kasa. A siyasance, Tinubu ya kafa harkar siyasan ce a yankin kudu maso yammacin Nijeriya. Kuma kamar yadda ne bayyana da bakinsa, ya kuduri burin zama shugaban kasa ne a dukkan tsawon rayuwarsa. Tabbas wannan burinasa ne ya sanya ya yi watsi da jam’iyyar ACN inda ya shiga hadaka da jam’iyyar APC, jam’iyyar da ke da asali daga yankin arewacin Nijeriya.

A wannan hadakar a gwamnatin da ta gabata, a ware wasu yankuna a yayin zaben shugabanin majalisar kasa, yayin da arewa ta samu shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, yankin kudu maso yamma suka samu mataimaki shugaban kasa da shugaban majalisar wakilai, muna kira ga zabbaben shugaban kasa da kada ya bi wannan hanyar.

Amma daga dukkan alamu, bangaren shugaban kasa basu kammala bukuwan lashe zabe ba, amma sai gashi har an fara gwagwamaryar neman shugabancin majalisan dattawa da kuma ta Wakilai.

Duk da cewa, a boye ake kamun kafar neman shugabancin majalisun biyu, amma al’umma na ganin yadda al’amurran ke tafiya, inda ake yi wa wasu ‘yan majalisar kamun kafa da yawa na amfanin da makaman da ke a hannun su wadanda suka hada da bukatar da yankunan suke cii na neman ayyukan cigaba, zamu ga wasu irin wadannan salon kamun kafar daga masu neman shugabancin majalisar kasa a nan gaba kada.

Akwai wasu tanade-tanade a cikin kundin tsarin mulkin kasa da aka tabbatar da cewa, ba a juya wa wani bangare ko jiha baya ba a harkar gudanar da kasa.  Baya ga tabbatar da shugaban kasa ya zabi Ministoci daga dukkan jihohin tarayyar kasar nan, tsarin mulki ya fayyace yadda za a kafa gwmanatin tarayya da ma na wasu ma’aikatun  gwamnati ta yadda za a tafi tare da kowa da kowa don samar da hadin kan kasa.

Da babu wannan tanadin da Tinubu yana da damar ya zabi ‘yan asalin jiharsa ta Legas su zama ministoci maimakon ya zaba daga jihohi 36 a tarayyar Nijeriya, sai dai a wuraren da ba a samu wadanda suka cancaci rike wani mukami ba daga wata jiha. Doka ta tanadi a rarraba mukamai a tsakanin shiyoyyin siyasa shida na kasar nan don kowa ya san ana damawa da shi. Don haka a kwai bukatar a yi takatsantsan wajen ganin kowacce bangare na kasa ya samu wakilci a dukkan bangarorin gudanar da mukin kasar nan gaba daya.

Hadin Kai
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.