• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sabbin Shugabannin Hisbah A Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Kananan Labarai
0
An Nada Sabbin Shugabannin Hisbah A Jihar Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hisbah a Jihar Katsina ta yi garanbawul a shugabancinta a matakin jiha tare da maye gurbin wasu sabbin shugabanni.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata samarwa da sakataren hukumar, ya fitar aka raba wa manema labarai a Katsina.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum A Kotu Kan Satar Dan Bunsuru 2
  • Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano

Sanarwar, ta ce tana sanar da al’umma game da wasu sauye-sauye da a ka samu a shugabancin Hisbah da suka shafi ofishin kwamandan jiha da magatakarda da kwamandan ladabtarwa da sauransu.

Hukumar ta ce ta maye gurbin tsohon kwamandan da Muhammad Rabi’u Garba, sai Abdullahi Yusuf a matsayin mataimakin kwamanda da kuma Muhammad Aminu Bello a matsayin magatakarda

Sauran sun hada da Muhammad Mahdi Rabi’u wanda ya maye gurbin kwamandan ladabtarwa sai kuma Abubakar Iliya a matsayin shugaban da’awa na Jihar Katsina.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Sanarwar ta ci gaba da bayanin cewa ta gode wa tsohon shugabanta na jiha Malam Hamisu Abubakar Imam a kan irin ci gaban da ya kawowa Hisbah a lokacinsa da kuma yi masa fatan nasara a rayuwarsa.

Haka kuma a jawabinsa sabon kwamandan Hisbah na Jihar Katsina, Muhammad Rabi’u Garba ya ba da tabbacin yin aiki tukuru ga al’ummar Jihar Katsina, da kuma kokarin kara bunkasa ayyukan Hisbah zuwa lunguna da sako-sako jihar.

Kazalika, ya taya zababben gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda murnar nasara da ya yi a zaben ranar Asabar 18 ga watan Maris, da yin addu’ar Allah SWT ya shige masa gaba a duk tsawon mulkinsa.

Sannan kuma yayi kira ga gwamnati mai zuwa da ta tabbatar da kafa hukumar Hisbah kamar yadda gwamnati mai barin gado ta Aminu Bello Masari ta yi.

Daga karshe shugaban ya taya dukkan Musulmai murnar shigowar watan Ramadan na shekara 1444 AH da fatan Allah SWT ya karbi dukkan ayyuka, da dacewa da alkairan da ke cikin wannan wata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaShugabbanin Hisbah
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Wani Mutum A Kotu Kan Satar Dan Bunsuru 2

Next Post

Fred M’membe:Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Za Ta Taimakawa Tabbatar Da Ci Gaban Duniya

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

2 weeks ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

2 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

2 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

3 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

9 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

9 months ago
Next Post
Fred M’membe:Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Za Ta Taimakawa Tabbatar Da Ci Gaban Duniya

Fred M’membe:Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Za Ta Taimakawa Tabbatar Da Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Hisbah

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.