• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya ce a mako mai zuwa ne majalisar za ta tantance sunayen ministoci bakwai da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika wa zauren majalisar domin tantance su.

Lawan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, gabanin dage zaman majalisar.

  • Buhari Ya Bukaci ‘Yan Majalisa Da Su Tabbatar Da Sabbin Sunayen Ministoci Da Ya Aike
  • An Fafata Da Lawan A Zaben Fidda Gwanin Sanatocin Yobe – Shugaban APC

“Za a tantance wadanda aka nada a matsayin ministoci ranar Laraba, mako mai zuwa”, in ji Lawan.

Shugaba Buhari, a wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da tantance sunayen ministoci bakwai.

Ya ce an gabatar da bukatar tabbatar da sashe na 147(2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 kamar yadda aka gyara.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Wadanda aka nada domin tantancewa sun hada da: Henry Ikechukwu Ikoh – Jihar Abia; Umana Okon Umana – Jihar Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- Jihar Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – Jihar Imo.

Sauran sun hada da Umar Ibrahim El-Yakub – Jihar Kano; Ademola Adewole Adegoroye – Jihar Ondo; da Odum Udi – Jihar Ribas.

Hakazalika, Majalisar Dattawa a jiya ta tabbatar da nadin Dr. Hale Gabriel Longpet (Plateau) a matsayin Kwamishinan Zabe na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Tabbatar da Longpet ya biyo bayan la’akari da rahoton kwamitin da ke kan al’amuran zabe.

Shugaban kwamitin, Sanata Kabiru Gaya (Kano ta Kudu), a jawabinsa, ya ce an gabatar da nadin Longpet ne bisa tanadin sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima).

Ya bayyana cewa wanda aka zaba a lokacin da ya gurfana gaban kwamitin domin tantancewa, ya bayar da bayani dangane da rayuwarsa, kwarewar aikinsa, dacewarsa, cancantarsa ​​da amincinsa na nadinsa a matsayin kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Ya ce mambobin Kwamitin sun yaba da kyakkyawan tsarin Karatu da kuma gamsassun amsoshi ga tambayoyin da aka gabatar.

Bayan haka, an tabbatar da wanda aka zaba a

zauren.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuharimajalisaMinistociSanatoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 3, Da Sace Wata Mata A Katsina

Next Post

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Related

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Labarai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

15 minutes ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

1 hour ago
Tinubu
Labarai

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

3 hours ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

15 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

16 hours ago
Next Post
Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
APC

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

June 14, 2025
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.