• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa

by Muhammad
3 years ago
Majalisar

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya ce a mako mai zuwa ne majalisar za ta tantance sunayen ministoci bakwai da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika wa zauren majalisar domin tantance su.

Lawan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, gabanin dage zaman majalisar.

  • Buhari Ya Bukaci ‘Yan Majalisa Da Su Tabbatar Da Sabbin Sunayen Ministoci Da Ya Aike
  • An Fafata Da Lawan A Zaben Fidda Gwanin Sanatocin Yobe – Shugaban APC

“Za a tantance wadanda aka nada a matsayin ministoci ranar Laraba, mako mai zuwa”, in ji Lawan.

Shugaba Buhari, a wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da tantance sunayen ministoci bakwai.

Ya ce an gabatar da bukatar tabbatar da sashe na 147(2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 kamar yadda aka gyara.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

Wadanda aka nada domin tantancewa sun hada da: Henry Ikechukwu Ikoh – Jihar Abia; Umana Okon Umana – Jihar Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- Jihar Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – Jihar Imo.

Sauran sun hada da Umar Ibrahim El-Yakub – Jihar Kano; Ademola Adewole Adegoroye – Jihar Ondo; da Odum Udi – Jihar Ribas.

Hakazalika, Majalisar Dattawa a jiya ta tabbatar da nadin Dr. Hale Gabriel Longpet (Plateau) a matsayin Kwamishinan Zabe na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Tabbatar da Longpet ya biyo bayan la’akari da rahoton kwamitin da ke kan al’amuran zabe.

Shugaban kwamitin, Sanata Kabiru Gaya (Kano ta Kudu), a jawabinsa, ya ce an gabatar da nadin Longpet ne bisa tanadin sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima).

Ya bayyana cewa wanda aka zaba a lokacin da ya gurfana gaban kwamitin domin tantancewa, ya bayar da bayani dangane da rayuwarsa, kwarewar aikinsa, dacewarsa, cancantarsa ​​da amincinsa na nadinsa a matsayin kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Ya ce mambobin Kwamitin sun yaba da kyakkyawan tsarin Karatu da kuma gamsassun amsoshi ga tambayoyin da aka gabatar.

Bayan haka, an tabbatar da wanda aka zaba a

zauren.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 
Labarai

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Labarai

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
Next Post
Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Majalisar

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.