ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa

by Muhammad
4 years ago
Majalisar

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya ce a mako mai zuwa ne majalisar za ta tantance sunayen ministoci bakwai da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika wa zauren majalisar domin tantance su.

Lawan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, gabanin dage zaman majalisar.

  • Buhari Ya Bukaci ‘Yan Majalisa Da Su Tabbatar Da Sabbin Sunayen Ministoci Da Ya Aike
  • An Fafata Da Lawan A Zaben Fidda Gwanin Sanatocin Yobe – Shugaban APC

“Za a tantance wadanda aka nada a matsayin ministoci ranar Laraba, mako mai zuwa”, in ji Lawan.

ADVERTISEMENT

Shugaba Buhari, a wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da tantance sunayen ministoci bakwai.

Ya ce an gabatar da bukatar tabbatar da sashe na 147(2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 kamar yadda aka gyara.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Wadanda aka nada domin tantancewa sun hada da: Henry Ikechukwu Ikoh – Jihar Abia; Umana Okon Umana – Jihar Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- Jihar Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – Jihar Imo.

Sauran sun hada da Umar Ibrahim El-Yakub – Jihar Kano; Ademola Adewole Adegoroye – Jihar Ondo; da Odum Udi – Jihar Ribas.

Hakazalika, Majalisar Dattawa a jiya ta tabbatar da nadin Dr. Hale Gabriel Longpet (Plateau) a matsayin Kwamishinan Zabe na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Tabbatar da Longpet ya biyo bayan la’akari da rahoton kwamitin da ke kan al’amuran zabe.

Shugaban kwamitin, Sanata Kabiru Gaya (Kano ta Kudu), a jawabinsa, ya ce an gabatar da nadin Longpet ne bisa tanadin sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima).

Ya bayyana cewa wanda aka zaba a lokacin da ya gurfana gaban kwamitin domin tantancewa, ya bayar da bayani dangane da rayuwarsa, kwarewar aikinsa, dacewarsa, cancantarsa ​​da amincinsa na nadinsa a matsayin kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Ya ce mambobin Kwamitin sun yaba da kyakkyawan tsarin Karatu da kuma gamsassun amsoshi ga tambayoyin da aka gabatar.

Bayan haka, an tabbatar da wanda aka zaba a

zauren.

Majalisar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.